Aminiya:
2025-03-25@14:30:29 GMT

’Yan gida daya sun yi wa ma’aurata dukan kawo wuka a Kano

Published: 10th, February 2025 GMT

An gurfanar da wasu mutum uku ’yan uwan juna kan yi wa wata matar aure da mijinta dukan kawo wuƙa a yankin Karamar Hukumar Gezawa da ke Jihar Kano.

An gurfanar da su ne a gaban Babbar Kotun Musulunci ta Gazawa kan zargin yi wa matar auren karaya uku a ƙafarta da hannunta bayan sun yi mata dukan kawo wuƙa tare da ji mata raunuka.

Sun kuma ƙuƙƙuje mijinta da ya yi ƙoƙarin ceton ta bayan shi ma suka lakaɗa masa duka.

Ana tuhumar su laifin yin kutse da yin barazana da haɗa kai wajen aikata laifi da ji wa mutane munanan raunuka.

’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe

Duk waɗanda ake zargin sun amsa laifukan da ake tuhumar su da aikatawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dukan kawo wuka

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano

Hukumar yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta kama wata mata ‘yar ƙasar Indiya mai suna Neetu Neetu, mai shekara 42, a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano, ɗauke da hodar iblis mai nauyin kilo 11 da aka ɓoye a cikin ledojin da ke kama da kwallon alawar cakulati. An cafke ta ne a yayin binciken shigowarta daga jirgin Qatar Airways daga Bangkok ta Vietnam da Doha.

Shugaban hukumar, Birgediya Janar Buba Marwa (Rtd), ya ce wannan kamun ya sake nuna yadda masu safarar kwayoyi ke amfani da ‘yan ƙasashen waje don kutsawa da miyagun kwayoyi cikin ƙasar. A cewarsa, NDLEA na ci gaba da daƙile irin wannan yunƙuri ta hanyar bayanan sirri da fasahohin zamani.

NDLEA Ta Gargadi Iyaye Kan Bayyanar Alawar Ƙwaya A Kano Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su 

A wani sumame a Kano, an kama Michael Ogundele dauke da tramadol guda 50,000 da aka boye a cikin bututun gas, yayin da a Gunduwawa aka cafke Sunday Ogar da kilogram 27 na wiwi. Haka zalika, an kama Khadijah Abdullahi a Lungun Bulala da kwalabe 424 na maganin tari mai sinadarin Kodin.

A Lagos kuwa, jami’an NDLEA sun kama mutane da dama da wiwi, da tramadol, da Kodin a Mushin, Apapa da Ikotun. NDLEA ta ci gaba da shirinta na wayar da kai a faɗin ƙasar, ciki har da makarantu da masallatai. Marwa ya yaba wa jajircewar jami’an hukumar, yana mai kira da su ci gaba da aiki da kwazo da rikon amana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar