’Yan gida daya sun yi wa ma’aurata dukan kawo wuka a Kano
Published: 10th, February 2025 GMT
An gurfanar da wasu mutum uku ’yan uwan juna kan yi wa wata matar aure da mijinta dukan kawo wuƙa a yankin Karamar Hukumar Gezawa da ke Jihar Kano.
An gurfanar da su ne a gaban Babbar Kotun Musulunci ta Gazawa kan zargin yi wa matar auren karaya uku a ƙafarta da hannunta bayan sun yi mata dukan kawo wuƙa tare da ji mata raunuka.
Sun kuma ƙuƙƙuje mijinta da ya yi ƙoƙarin ceton ta bayan shi ma suka lakaɗa masa duka.
Ana tuhumar su laifin yin kutse da yin barazana da haɗa kai wajen aikata laifi da ji wa mutane munanan raunuka.
’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗeDuk waɗanda ake zargin sun amsa laifukan da ake tuhumar su da aikatawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dukan kawo wuka
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
Al’ummar Mauritaniya sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da yakin da ake yi a Gaza
A karkashin taken “An rusa Gaza” kuma goyon bayan al’umma ga Falasdinawa abu ne da ya zama wajibi, ba zabi ba, mazauna birnin Nouakchott fadar mulkin kasar Mauritaniya sun gudanar da zanga-zanga domin jaddada bukatar musulmi a ko’ina a duniya su goyi bayan gwagwarmayar da ake yi a Zirin Gaza.
Zanga-zangar dai ta samu halartar kungiyoyin ‘yan jaridu da sauran kungiyoyi da dama, wadanda suka bayyana Allah wadai da shirun da manyan kasashen duniya suka yi, tare da sukar su kan goyon bayan sojojin mamayar Isra’ila.
Wani sheikhin malami dan kasar Mauritaniya ya ce: “Sun sanar da mu irin wannan gagarumin aiki, Allah Ya saka musu da alheri kan irin wannan zanga-zangar da suke yi na goyon bayan wadanda ake zalunta ta hanyar kashe mata da yara da kuma tsofaffi da suke yunkurin kare hakkokinsu.
Masu zanga-zangar sun yi kira da a yanke alaka tsakanin kasarsu da Amurka da duk masu goyon bayan yahudawan sahayoniyya a yakin da suke yi na neman shafe Falasdinawa daga kan doron kasa tare da azabtar da su da masifar yunwa a zirin Gaza.