Aminiya:
2025-03-23@22:46:15 GMT

’Yan daba sun ƙona gine-ginen makaranta a Binuwai

Published: 10th, February 2025 GMT

Wasu ’yan daba sun gine-ginen makaranta a yankin Okpoga da ke Karamar Hukumar Okpogwu da ke Jihar.

Ɓata-garin sun ƙona gine-ginen ne a Makarantar Sakandaren Central UBE da ke Ogwu-Okpoga da kuma Makarantar Ƙaramar Sakandare s ake Obossa.

Wani shaida ya bayyana wa wakilinmu cewa a makon da ya gabata ne ’yan daban suka yi wannan aika-aika.

Shaidan wanda bai amince a bayyana sunansa ba, ya yi zargin wata manufar siyasa ce ta sa ’yan daban suka cinna wa gine-ginen wuta. Ya bayyana damuwa kan yawaitar irin wannan aika-aika a ’yan kwanakin nan.

Kokarinmu ma ji daga kakakin ’yan sanda ta Jihar Binuwai, Catherine Aneneh, bai yi nasara ba, saboda mun kira ta a waya ba ta shiga ba.

’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya?

Amma a ƙarshen mako ɗan Majalisar Dattawa mai wakiltar Binuwai ta Kudu kuma Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dattawa, Sanata Abba Moroh, ya ziyarci makarantun da abun ya shafa a ƙarshen mako.

Abba Moroh ya yi tir da lamarin tare da mamakin dalilin ƙona cibiyoyin ilimi da ake rainon manyan gobe.

Daga nan sai ya yi alƙawarin sake gina ajujuwan yana mai kira ga al’ummar yankin da su tashi domin kare ababen more rayuwar da aka samar musu.

Dan majalisar ya kuma ziyarci babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Yankin Okpoga, inda ya jinjiya musu bisa ƙoƙarinsu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Sai dai ya koka bisa mummunan halin da ofishin yake ciki, sannan ya yi alƙawarin yi masa kwaskwarima.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan daba Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran

Kasar Rasha ta bayyana cewa dole Moscow da Beijing su shiga shawarwarin tattaunawar nukiliya da Iran.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta bayyana cewa, Moscow a shirye take ta samar da ingantacciyar hadin gwiwa da dukkan bangarorin kan batun yarjejeniyar nukiliyar Iran. “

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa ya aike da wasika zuwa Tehran domin fara tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran; yayin da shi da kansa ya fice daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a wa’adinsa na farko.

A halin da ake ciki dai ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.

Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) ranar Alhamis.

Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.

Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”

Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.

A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam
  • ’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano
  • Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa