Gwamnatin tarayya ta yabawa gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa bisa kammala aikin kaso 97 na ayyukan tituna da ya gada daga gwamnatin da ta gabata a jihar.

Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a garin Auyo yayin kaddamar da shirin wayar da kan jama’a da gwamnati da al’umma a jihar Jigawa.

Badaru wanda ya nuna gamsuwarsa matuka, ya ce gwamnatin jihar ta kammala ayyukan tituna guda 23 cikin 26 da ta gada.

Ya kara da cewa sauran ayyukan tituna guda uku sun kusa kammaluwa domin amfanin al’umma da ci gaban tattalin arzikin jihar.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati mai ci za ta kawo karin ayyukan raya kasa, don haka akwai bukatar bai wa gwamnatin jihar duk wani goyon baya da hadin kai don cimma buri da muradin al’umma.

A nasa jawabin Gwamna Umar Namadi ya ce gwamnati mai ci ta zabo sama da makarantu dubu daya da tamanin da za su ci gajiyar shirin bunkasa ilimi tare da hadin gwiwar kungiyar New Globe.

A cewarsa, an zabo makarantun ashirin da  biyu a karamar hukumar Auyo da nufin inganta koyo da koyarwa a makarantun gwamnati.

Namadi ya yi nuni da cewa, gwamnatinsa ta bullo da tsare-tsare a karkashin ajandarta guda 12 na samun babban jigawa.

Shi ma da yake jawabi, Sanata mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Yamma, Ambasada Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya ce sabon shirin da aka bullo da shi zai kara kusantar da mutane ga gwamnati tare da aiwatar da ayyukan da za su yi tasiri ga rayuwar al’umma.

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Injiniya Aminu Usman da kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim da jami’an gwamnati da kuma ‘yan majalisar dokoki na kasa da na jiha.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa

Rundunar ‘Yansandan Jihar Adamawa ta kama Umar Shaibu bisa zargin cin zarafin wata mata a yankin Jimeta a jihar. An kama Shaibu ne bayan wani bidiyo mai tayar da hankali ya yadu a kafafen sada zumunta, kamar yadda Jami’in hulda da Jama’a na ‘Yansandan Jihar Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ya bayyana. Salamatu Yakubu, matar mai shekaru 22 daga Angwan Tana, an ce wanda ake zargin ya yi ma ta dukan jakin ne mai tsanani, Shaibu, wanda ake cewa shi ne dan uwanta.

Wannan lamarin ya janyo zarge-zargen daga al’umma da kuma kiran da aka yi wa Yansanda daga mutanen gari, da kungiyoyin fararen hula, da sauran masu rajin kare hakkin bil’adama domin a kama wanda ake zargi.

Ƴansanda Sun Kama  Ɓarayin Waya Masu Amfani Da Keke Napep A Adamawa An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

An kama Shaibu ne tare da taimakon al’umma ta hanyar dabarun kula da tsaro na cikin gari. An tura matar da aka yi wa dukan cutar zuwa asibiti domin samun kulawar likita.

A halin yanzu, wanda ake zargin yana tsare a sashin binciken laifuka na musamman na Jihar (SCID) a sashin kula da mata domin a gudanar da cikakken bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu. Rundunar Yansandan ta tabbatar wa da jama’a cewa za a binciki lamarin sosai kuma wanda ake zargi zai fuskanci shari’a bisa dokokin da suka dace.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci