Gwamnatin tarayya ta yabawa gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa bisa kammala aikin kaso 97 na ayyukan tituna da ya gada daga gwamnatin da ta gabata a jihar.

Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a garin Auyo yayin kaddamar da shirin wayar da kan jama’a da gwamnati da al’umma a jihar Jigawa.

Badaru wanda ya nuna gamsuwarsa matuka, ya ce gwamnatin jihar ta kammala ayyukan tituna guda 23 cikin 26 da ta gada.

Ya kara da cewa sauran ayyukan tituna guda uku sun kusa kammaluwa domin amfanin al’umma da ci gaban tattalin arzikin jihar.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati mai ci za ta kawo karin ayyukan raya kasa, don haka akwai bukatar bai wa gwamnatin jihar duk wani goyon baya da hadin kai don cimma buri da muradin al’umma.

A nasa jawabin Gwamna Umar Namadi ya ce gwamnati mai ci ta zabo sama da makarantu dubu daya da tamanin da za su ci gajiyar shirin bunkasa ilimi tare da hadin gwiwar kungiyar New Globe.

A cewarsa, an zabo makarantun ashirin da  biyu a karamar hukumar Auyo da nufin inganta koyo da koyarwa a makarantun gwamnati.

Namadi ya yi nuni da cewa, gwamnatinsa ta bullo da tsare-tsare a karkashin ajandarta guda 12 na samun babban jigawa.

Shi ma da yake jawabi, Sanata mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Yamma, Ambasada Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya ce sabon shirin da aka bullo da shi zai kara kusantar da mutane ga gwamnati tare da aiwatar da ayyukan da za su yi tasiri ga rayuwar al’umma.

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Injiniya Aminu Usman da kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim da jami’an gwamnati da kuma ‘yan majalisar dokoki na kasa da na jiha.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja

Wata tanka ɗauke da man fetur ta kama da wuta yayin da ta ke sauke mai a gidan mai na A.A. Rano da ke Kontagora, a Jihar Neja.

Lamarin ya faru ne da da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Lahadi kusa da Asibitin Gaba.

Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne yayin da ake sauke man fetur, lamarin da ya jefa jama’a cikin fargaba kasancewar sauran tankunan mai maƙare suke da fetur.

Jami’an kashe gobara sun garzaya wajen don shawo kan lamarin, amma har yanzu wutar na ci gaba da yaɗuwa.

“Babu wanda aka ruwaito ya rasa ransa, amma mutane sun tsere domin tsira da rayukansu,” in ji wani mutum, mai suna Abba Mohammed.

Ƙoƙarin jin ta bakin Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, ya ci tura zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari