Ɗalibi ya kashe abokin karatunsu da gatari a Nasarawa
Published: 10th, February 2025 GMT
Wani ɗalibi a Kwalejin Kimiyya da Ƙere-kere ta Tarayya da ke Jihar Nasarawa ya yi wa abokin karatunsa kisan gilla ta hanyar amfani da wuƙa da gatari.
Rundunar ’Yan Sanda Jihar Nasarawa ta ce ɗalibin da ya yi kisan gillar ɗan ajin ND2 a Fannin Aikin Banki da Hadahadar Kuɗaɗe ne a Kwalejin kuma yana hannunta, yana amsa tambayoyi.
Ta bayyana cewa ya amsa laifin tare da shaida wa masu bincike cewa ya yi amfani da wuƙa da kuma gatari wajen halaka abokin nasa a gidan da suke haya bayan wata hatsaniya a tsakaninsu.
Kakakin rundunar, Rahman Nansel, ya bayyana cewa jami’an rundunar sun kai ɗauki ne bayan matar da ɗaliban ke haya a gidanta, Mercy-Bassey, ta sanar da rundunar cewa rikici ya ɓarke a tsakanin maƙwabtakan nata.
Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe ’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan dabaYa ce ko da jami’an suka isa, sai suka tarar da gawar ɗaya ɗalibin ɗan abin ND2 a Fannin Kimiyyar Kwamfuta kwance a cikin jini a cikin ɗakin.
Jami’in ya ce an garzaya da shi Babban Asibitin Nasarawa, inda likitoci suka sanar cewa rai ya riga ya yi halinsa saboda tsananin raunukan da ya samu.
Ya ce Kwamishinan ’yan sandan jihar, Shettima Jauro-Mohammed ya ba da umarnin a tsananta bincike a kan lamarin.
Tuni aka ɗauke makaman da sauran abubuwan da aka iske a wurin da abin ya faru a matsayin shaida, gawar kuma an kai ta ɗakin ajiyar gawa domin gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda gatari kwaleji
এছাড়াও পড়ুন:
Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
Aƙalla fasinjoji huɗu ne suka mutu yayin da wasu huɗu suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a ƙarƙashin wata motar kasuwanci a ƙaramar hukumar Biu ta Jihar Borno.
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta tabbatar ta afkuwar lamarin.
Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a BenuweMajiyoyin leƙen asiri sun shaidawa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne a ranar 19 ga Maris, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana a lokacin da wata mota ƙirar Golf 3 ta Wakil Fari ta tashi daga garin Kimba zuwa garin Biu.
Bayan sun isa mahaɗar Sabon Garin Kimba, motar ta taka wata nakiya (IED), wanda ya kai ga fashewa da ta kashe fasinjoji mata uku da fasinja namiji guda nan take.
Majiyar na cewar wasu fasinjoji hudu kuma sun sami raunuka daban-dabam kuma nan da nan an kai su babban asibitin Biu don yi musu jinya.
Daga bisani likitoci sun tabbatar da mutuwar wadancan mutane huɗu sannan aka ajiye su a ɗakin ajiyar gawa na asibitin kafin a miƙa su ga ’yan uwansu don yi musu jana’iza.
Bincike na farko ya nuna cewa ’yan ta’addar ISWAP ne suka dasa waɗannan bama-bamai (IEDs) a tunanin sojoji za su taka.
Jami’an soji sun tabbatar da faruwar hakan, tare da duba ƙarin barazanar da ake fuskanta daga wadannan ‘yan ta’addan don tabbatar da tsaro ga masu amfani da hanya.
Hukumomi sun kuma ƙaddamar da gangamin wayar da kan al’umma kan haɗarin bama-bamai da ba su fashe ba, don kaucewa faruwar lamari irin ya hakan.