Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Dauki Nauyin Aurar Da Mata 300 Kafin Azumi
Published: 10th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kebbi, ta kammala shirye-shiryen gudanar da daurin auren mata dari uku a karshen watan Fabrairun wannan shekara.
Da yake zantawa da manema labarai da yammacin Lahadi, shugaban babban kwamitin kuma tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar, Suleiman Muhammad Argungu, ya bayyana cewa, nasarar daurin auren da aka yi a shekarar da ta gabata, wanda gidauniyar NANAS ta uwargidan Gwamnan, Hajiya Nafisa ta shirya, ya sanya gwamnatin ta sami kwarin gwiwar daukar nauyin aurar da wasu rukunin a wannan shekarar.
A cewar Shugaban kwamitin, za a aurar da mutane 600 marasa galihu ba tare da la’akari da addini, kabilanci da siyasa ba a tsarin gwamnati.
Ya ce, an kafa kwamitocin tantancewa a dukkan kananan hukumomi 21 domin zabar ma’auratan da suka cancanta bisa ka’idojin da aka gindaya wadanda suka hada da tabbacin ango yana da abin yi do daukar nauyin iyalansa, da kuma matsugunin da za su zauna.
Suleman Argungu, ya bayyana cewa, dukkan ma’auratan za a yi musu gwajin lafiya na tilas, ciki har da gwajin kwayar cutamai karya garkuwar jiki ta HIV, da kwayoyin halitta na Genotype.
Za a biya Naira 180,000 a matsayin sadaki ga kowace amarya, wanda ya kama jimillar Naira miliyan 54, tare da kayan daki, da suka katifa, gado da kuma kayan amfanin gida.
Daga Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Aurar Da Mata 300
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
Shugaba Bola Tinubu ya bayyana bakin cikinsa kan harin da aka kai Jihar Filato wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 40.
A cikin wata sanarwa, Shugaban kasa ya la’anci wannan tashin hankali tare da mika ta’aziyyarsa ga Gwamna Caleb Mutfwang, Gwamnatin Jihar, da al’ummar Filato.
Sanarwar da Mai ba Shugaban Kasa shawara na musamman kan Harkokin Yada Labarai Mista Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, ta bukaci Gwamnan da ya nuna cikakken ikonsa wajen warware rikicin da tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.
Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin soyayya da hadin kai a maimakon bambancin addini da kabila.
Ya bukaci shugabannin al’umma, da na addinai, da ma na siyasa a ciki da wajen jihar, da su hada kai domin kawo karshen ramuwar gayya da rikice-rikicen da suka jima suna addabar al’umma.
“Ya zaman wajibi a kawo karshen rikicin da ke faruwa tsakanin al’umma a Jihar Filato wanda ya samo asali daga rashin fahimta tsakanin kabilu da addinai daban-daban.” In ji Shugaba Tinubu.
“Na umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan wannan rikici, da gano wadanda ke da hannu a shirya wadannan ayyukan tashin hankali. Ba za mu amince da wannan barna da hare-haren ramuwar gayya ba. Ya isa haka.
Ya ce Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da ba Gwamna Mutfwang da Gwamnatin Jihar Filato goyon baya wajen karfafa tattaunawa, inganta zaman tare, da tabbatar da adalci don magance wannan rikici har abada.
Daga Bello Wakili