HausaTv:
2025-04-18@22:37:46 GMT

Sam Nujoma Wanda Ya Kafa kasar Namibia Ya Rasu Yana Dan Shekara 95 A Duniya

Published: 10th, February 2025 GMT

Sam Nujoma, dan gwagwarmaya neman yencin kasar Namibiya karkashin gwamnatin wariyar launin fata ta Afrika ta kudu, ya rasu a jiya Lahadi kamar yanda gwamnatin kasar ta Namibi a ta bada sanarwa.

Shugaban kasar ta Namibia mai ci, Nangola Mbumba ya ce tsohon shugaban kasar ya na jinya a as wani asbiti a babban birnin kasar  Windhoek  na kimani makonni 3 amma rai yayi halinsa a daren Asabar da ta gabata ya na dan shekara 95.

Shafin yanar gizo na Labarai ‘Africanews’ ya bayyana cewa kasar Namibia ta sami yencin kanta ne daga hannun gwamnatin wariya ta Afirka ta kudu a shekara 1990. Sannan Nujoma ya zama shugaban kasar na farko na tsawon shekaru 15. Sannan aka zabi shugaba mai ci.

Shugaban bai bayyana cutar da ta kashe tsohon shugaban kasar kuma wanda ya samarwa kasar Yencin kanta ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya fitar da wata sanarwa mai ƙarfi game da yiwuwar dawowar wasu shugabannin siyasa cikin jam’iyyar. A lokacin ganawar da manema labarai a Kano, Abbas ya bayyana cewa APC ba za ta karɓi mutane da hukumomin yaƙi da cin hanci kamar EFCC da ICPC ke bincike ba.

Wannan sanarwa ta zo ne a yayin da jita-jita da ake cewa wasu daga cikin mambobin jam’iyyar NNPP, musamman waɗanda ke cikin rukuni na Kwankwasiyya, suna duba yiwuwar komawa APC.

El-rufa’i Ba Zai Halarci Taron Jam’iyyar APC Na Kasa Ba, Kuma Ganduje Na Nan A Shugabanci  NNPP Ta Mutu, Kwankwaso Zai Sake Dawowa APC – Ganduje

Abbas ya bayyana cewa duk wanda ke son dawo wa jam’iyyar dole ne ya nemi afuwa daga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, bisa maganganun cin mutunci da aka yi a baya akan su da jam’iyyar.

Masu fashin baƙin siyasa na ganin cewa wannan magana ta Abbas tana nufin shugaban Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ake zargin yana cikin tattaunawar yiwuwar sauya sheƙa. Wannan furucin na shugaban APC na Kano ya janyo muhawara game da yadda siyasa da daidaiton ra’ayi za su iya faruwa a cikin tsarin siyasar Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar
  • UEFA: Mbappe Zai Jagoranci Real Madrid Yayin Da Ta Ke Fatan Kafa Sabon Tarihi A Santiago