Aminiya:
2025-02-21@14:24:18 GMT

Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga

Published: 10th, February 2025 GMT

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Dare, ya bayyana cewa sharaɗinsa na sulhu da ’yan bindiga shi ne kawai su daina kashe-kashe su zubar da makamai sannan su miƙa wuya.

A baya dai Gwamna Dare ya sha nanata cewa ba zai yi sulhu da ’yan fashin daji ba.

Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri

Ko a watan Yulin 2024, sai da wani mai magana da yawunsa, Alhaji Faruk Ahmad, ya bayyana cewa babu wani matsin lamba da zai sa gwamnatinsu ta yi sulhu da ’yan ta’addan.

Ya kuma jaddada cewa mataki ɗaya da gwamnatin ta ɗauka wanda kuma yana haifar da ɗa mai ido shi ne yaƙar ’yan bindigar amma babu batun sulhu.

Sai dai a hirarsa da BBC, Gwamnan ya bayyana cewa ba wai ba za a iya yin sulhu da ’yan bindigar ba ne, “amma ko da za ka yi sulhu ka yi shi a kan gaskiya, ai.

“Akwai da yawa waɗanda aka cutar da su, wasu an kashe iyayensu wasu matansu, saboda haka sai a duba me za a yi masu saboda sun rasa dukiyarsu, bawai kullum a riƙa fitfita ƴanbindiga ba,” in ji Dauda.

Ya ƙara da cewa sai ’yan bindigar sun daina kashe mutane kuma sun ajiye makamansu sannan za a iya yin sulhu da su.

Gwamna Dauda ya bayyana cewa suna samun nasara a yaƙin da suke da ƴanbindiga, “An kashe ’yan ta’adda fiye da 50 a ranar Juma’a a garin Tingar Fulani, wajen Zurmi da Shinkafi.

“Akwai manya-manyan kachalloli da yanzu haka sun tafi lahira, waɗanda suke tare da Bello Turji, akwai Sani Mainasara da Sani Black da Kachallah Auta, Audu Gajere da Kabiru Jangero, Dangajere da makamantansu, duk an hallaka su,” a cewar Dauda Lawal.

Gwamnan ya ce wannan nasara da ake samu za a ci gaba da samunta “har sai na kai ƙarshen lamarin. Ko dai su ajiye makamansu ko kuma mu ba za mu bar su ba.”

Matsin lamba ya sa ’yan bindiga neman sulhu — Makama

Fitaccen mai sharhi kuma masani akan sha’anin tsaro Zagazola Makama ya bayyana cewa matsin lamba da sojoji ke yi wa ’yan bindiga ya sa suke neman sulhu.

Zagazola ya bayyana haka a shafinsa yayin da yake sharhi akan wani faifan bidiyo da yake yawo, inda aka ji Bello Turji da wani shahararren malami a Zamfara, suna tattaunawa akan yadda ɗan bindigar zai ajiye makamai.

A baya-bayan nan, manyan ’yan bindiga da dama sun bayyana aniyarsu ta ajiye makamai sun rungumi zaman lafiya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Dauda Lawal Dare Jihar Zamfara ya bayyana cewa yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara

Wani sabon rikici ya sake kunno kai a tsakanin manyan jam’iyyun siyasa biyu a Jihar Zamfara.

Rigimar wadda ta kunno tsakanin APC da PDP ta samo asali ne tun bayan da wasu matasa suka yi yunƙurin hana wani taro na ɗan Majalisar Wakilai da za a gudanar a garin Maru.

Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno

Hakan ya sa Gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta ɗauki wani matakin da take ganin zai kawo lafawar lamarin.

Sai dai kuma matakin da gwamnatin ta ɗauka bai yi wa jam’iyyar APC daɗi ba, inda ta nuna rashin gamsuwa tare da zargin ba a yi mata adalci ba saboda kasancewarta jam’iyyar adawa.

A bayan nan ne Gwamnatin Zamfara ta dakatar da duk wasu tarukan siyasa a jihar saboda samar da zaman lafiya da daidaito.

A bayanin da mai taimaka wa Gwamnan Zamfara kan kafafen yaɗa labarai, Mustapha Jafaru Kaura ya fitar, ya ce matakin na zuwa ne bayan hatsaniyar da aka samu a tsakanin jam’iyyun PDP da APC a Ƙaramar Hukumar Maru.

“Duk wani taron siyasa da zagaye an dakatar da shi a wannan lokaci, la’akari da abin da ya faru a Maru inda aka samu salwantar rayuka da ƙone-ƙonen dukiya.”

Hadimin gwamnan ya ce an ɗauki matakin ne ba don a musguna wa wasu ba face sai don samar da zaman lafiya kuma dokar da aka sanya ta wucin gadi ce.

Jam’iyyar APC a Zamfara ta nuna rashin gamsuwar ta kan matsayar da gwamnatin ta ɗauka tana mai zargin cewa gwamnatin ta mayar da hankali kan abin da ba shi ne ya fi ba.

Wata sanarwa da APC ta fitar ta bayyana cewa dole ne hukumar ’yan sanda a jiha ta kama waɗanda suka kai farmaki ga magoya bayanta a yayin da suke gudanar da kowane taro.

Jam’iyyar ta ce gargaɗin ya zama wajibi ganin yadda ‘yan sanda suka fita batun koken da aka gabatar musu a rubuce har guda uku.

“A cikin matasan da muke zargi, ’yan bangar siyasa daga jam’iyyar PDP da ’yan sa kai ne suka kawo farmaki a wurin rabon kayan ɗan Majalisar Wakilai na Maru da Bungudu, Honarabul Abdulmalik Zubairu Bungudu.

“Ɓatagarin sun laɓe ne kan hanyar Gusau zuwa Bungudu inda suka kai harin kan magoya bayan APC sannan suka lalata ababe hawa da dama.

Sakataren yaɗa labarai na APC a Zamfara, Yusuf Idris Gusau ya yi tir da lamarin, yana mai kiran jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

Idris Gusau ya ce “muddin ba haka ba zai sa mu riƙa kare kansu kan kowane mutum da ya nemi cin zarafinsu.”

Sakataren ya nemi magoya bayansu da su kwantar da hankali domin za a tabbatar da an yi adalci ga waɗanda aka ji wa rauni ko aka ɓarnata dukiyoyinsu.

“A matsayinmu na masu son zaman lafiyar Jihar Zamfara ba za mu bari a yi amfani da mu don kawo hargitsi ba kamar yadda jam’iyyar PDP ke kitsawa,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
  • Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
  • Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara