Aminiya:
2025-03-25@20:11:28 GMT

Dalilin da na ziyarci Obasanjo — Atiku

Published: 10th, February 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya bayyana dalilin ziyarar da ya kai wa tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a wannan Litinin ɗin.

Aminiya ta ruwaito cewa, da misalin ƙarfe 12:36 na yau Litinin ce tawagar da Atikun ya jagoranta ta isa gidan tsohon Shugaban Ƙasar da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya samu rakiyar tsohon gwamnan Jihar Kuros Riba, Liyel Imoke da takwaransa na Sakkwato, Sanata Aminu Tambuwal haɗi da ɗan Majalisar Dattawa mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya, Sanata Abdul Ningi.

Bayanai sun ce an shafe tsawon sa’a ɗaya da rabi ana ganawar wadda aka yi ta a bayan labule.

Sai dai da yake zantawa da manema labarai da misalin ƙarfe 2:11, Atiku ya bayyana cewa ziyarar ban girma ce kawai ta kawo shi wurin ubangidan nasa.

Haka kuma duk da tsananta ƙwaƙƙwafi da manema labaran suka yi, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ce ba zai ce uffan ba dangane da duk wani batu da ya shafi siyasa.

“Ziyarar ban girma ce ta kawo ni saboda haka ba zan ce komai a kan abin da ya shafi siyasa ba,” in ji Atiku.

Atiku ya kasance mataimaki ga Obasanjo daga watan Mayun 1997 zuwa Mayun 2007.

A bayan nan dai Atiku wanda ke muradin kujerar Shugaban Nijeriya ya yi ganawa daban-daban kan abin da ake zargin shirye-shiryen tunkarar Zaɓen 2027.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar Zaɓen 2027 ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya

Wasu manyan ’yan Nijeriya da suka tafi Umarah sun yi wa Gwamnan Katsina Dikko Umar Radda ta’aziyya a Saudiyya.

A safiyar Lahadi ce dai Allah Ya karɓi rayuwar mahaifiyar Gwamnan, Hajiya Safara’u Umaru Baribari bayan shafe tsawon lokaci tana jinya a Jihar Katsina.

Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci

Bayan rasuwar ce gwamnoni da wasu fitattun ’yan siyasa da a halin yanzu suna ƙasa mai tsarki suka kai wa Gwamna Radda ziyara domin jajanta masa dangane da wannan babban rashi.

Daga cikin gwamnonin akwai Mohammed Umar Bago na Jihar Neja, da Farfesa Babagana Zulum na Jihar Borno da Gwamna Uba Sani na Kaduna, da Dauda Lawal Dare na Zamfara da kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe

Sauran fitattun ’yan siyasar da suka ziyarci Gwamna Radda sun haɗa da Shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, da tsohon Gwamnan Bauchi, Ahmed Mu’azu.

Akwai kuma fitaccen attajirin nan kuma ɗan kasuwa, Alhaji Dahiru Mangal da kuma tauraron tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Super Eagles, Ahmed Musa da su ma suka jajanta wa gwamnan a kan rashin.

Dukkansu sun bayyana alhini tare da roƙon Allah Ya jiƙan Hajiya Safara’u Ya sa ta huta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
  • Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba
  • Yawan Ziyarar Da ‘Yan Siyasa Da ‘Yan Kasuwar Amurka Ke Kawowa Sin Ya Zo Da Mamaki
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027