Janar Bakiri Yace: Sojojin Iran A Shirye Suka Fiye Da Ko Wani Lokaci
Published: 10th, February 2025 GMT
Babban hafsan hafsishin sojojin Iran Manjo Janar Muhammad Bakri ya bayyana cewa sojojin Iran a shirye suke fiye da ko wani lokaci don kare JMI daga makiyanta.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Bakiri ya bayyana haka ne a lokacinda yake tattaki na bukukuwan cika shekaru 46 da nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a nan birnin Tehran a safiyar yau Litinin.
Ya ce: Halin da sojojin JMI suke ciki yafi na ko wani lokacin kyau, don haka a shirye suke su gudanar da ayyukansu a duk lokacinda bukatar haka ta taso.
Dangane da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka kuma, Janar Bakiri ya bayyana cewa, jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya rika ya bayyana matsayin JMI dangane da haka.
Kafin haka dai Jagoran ya bayyana cewa Iran a baya ta tattauna da manya-manyan kasashe 6 a duniya daga cikin har da kasar Amurka, an cimma yarjeniyar a tsakanin kasashen mai suna JCPOA, amma shekaru biyu bayan haka shugaban kasar Amurka mai ci, Donal Trump a shekara ta 2018 ya yi watsi da yarjeniyar, ya kuma dorawa Iran sabbin takunkuman tattalin arziki mafi tsanani a kan kasar.
Don haka sake shiga tattaunawa da irin wannan mutum babu mutunci, ba abu ne wanda mai hankali zai amince ba, kuma wulakanci ne ga kasar Iran.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.
Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance wajen asibiti.
Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.
Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.
Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.