HausaTv:
2025-04-14@23:47:05 GMT

Janar Bakiri Yace: Sojojin Iran A Shirye Suka Fiye Da Ko Wani Lokaci

Published: 10th, February 2025 GMT

Babban hafsan hafsishin sojojin Iran Manjo Janar Muhammad Bakri ya bayyana cewa sojojin Iran a shirye suke fiye da ko wani lokaci don kare JMI daga makiyanta.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Bakiri ya bayyana haka ne a lokacinda yake tattaki na bukukuwan cika shekaru 46 da nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a nan birnin Tehran a safiyar yau Litinin.

Ya ce: Halin da sojojin JMI suke ciki yafi na ko wani lokacin kyau, don haka a shirye suke su gudanar da ayyukansu a duk lokacinda bukatar haka ta taso.

Dangane da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka kuma, Janar Bakiri ya bayyana cewa, jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya rika ya bayyana matsayin JMI dangane da haka.

Kafin haka dai Jagoran ya bayyana cewa Iran a baya ta tattauna da manya-manyan kasashe 6 a duniya daga cikin har da kasar Amurka, an cimma yarjeniyar a tsakanin kasashen mai suna JCPOA, amma shekaru biyu bayan haka shugaban kasar Amurka mai ci, Donal Trump a shekara ta 2018 ya yi watsi da yarjeniyar, ya kuma dorawa Iran sabbin takunkuman tattalin arziki mafi tsanani a kan kasar.

Don haka sake shiga tattaunawa da irin wannan mutum babu mutunci, ba abu ne wanda mai hankali zai amince ba, kuma wulakanci ne ga kasar Iran.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari

Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.

 Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa  lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance  wajen asibiti.

Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.

Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.

 Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro