NUC Ta Dakatar Da Bayar Da Lasisin Gina Sabbin Jami’o’i Masu Zaman Kansu.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla

Kungiyar da ke sa ido da kare hakkin dan adam ta Syria (SOHR) ta fitar da fayafan bidiyo guda hudu da ke dauke da hotunan azabtarwa da kisa da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin kasar  karkashin kungiyar Tahrir Sham  suke aiwatarwa a kan fararen hula tsiraru marasa rinjaye a kasar.

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayyana a ranar Lahadi cewa, ta samu faifan bidiyo guda hudu ne da ke nuna yadda ake aiwatar da hukuncin kisa kan wasu matasa da ba sa dauke da makamai daga ‘yan Alawiyya, da jami’an tsaro suka aiwatar a kauyen al-Shir da ke yankin Latakia a ranar 7 ga watan Maris.

A cewar kungiyar, faifan bidiyon ya kara tabbatar da yadda aka aiwatar da kisan gillar da aka yi a yankunan gabar tekun Syria da kuma wadanda suka aikata hakan a kan fararen hula.

A cikin faifan bidiyo na farko ya nuna wasu matasa biyu sun durkusa a kasa yayin da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria  suke zaginsu tare da lakada musu matsanancin duka, duk kuwa da ikirarin da suka yi na cewa ba su aikata wani laifi ba.

A cikin wani faifan bidiyo na biyu, an nuna yadda aka azabtar da wasu fararen hula hudu  ciki har da tsofaffi biyu, da kuma tilasta wa daya daga cikinsu sumbaci takalmin wani jami’in tsaro.

Kaset na uku ya nuna irin mumunan duka da aka yi wa fararen hula da bindigogi da karafa kafin daga baya kuma duk aka kashe su.

Dukkanin wadanda suka aikata wadannan munannan laifuka dai sabbin jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da kungiyar Tahrir Sham mai dangantaka da kungiyar Alqaida ta kafa a Syria bayan hambarar da gwamnatin Bashar Assad.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar
  • Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa