Aminiya:
2025-04-14@23:44:30 GMT

’Yan bindiga sun kashe fasto a Gombe

Published: 10th, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wani fasto, Rabaran Bala Galadima yayin harin da suka kai garin Lubo da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba a Jihar Gombe.

Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun kuma yi fashin kuɗi har Naira dubu 300 a yayin harin da suka kai cikin dare wayewar gari Lahadi.

Wani mazaunin garin ya bayyana cewa maharan, waɗanda sun kai takwas, sun kai farmakin ne da misalin karfe 1 zuwa 3 na dare, inda suka firgita jama’a da harbe-harbe kafin su kutsa cikin gidan wani mutum mai suna Musa Puma.

Majiyar ta ce maharan sun rutsa matar gidan da bindiga inda suka karbi kuɗi naira dubu dari 300 tare da yin garkuwa da ɗaya daga cikin ’ya’yansu da kuma barazanar kashe shi muddin aka yi musu tirjiya.

Shi kuwa Faston Cocin ECWA na garin Lubo, Rabaren Bala Galadima, ya rasa ransa ne bayan da maharan suka harbe shi a gadon baya a gidansa, lamarin da ya girgiza al’ummar garin.

Gwamnati Ta Yi Allah Wadai

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allah wadai da kisan Rabaren Bala Galadima, tare da bayyana alhininsa kan wannan aika-aika.

A wata sanarwa da Babban Daraktan Yada Labarai na Gwamnatin Jihar, Isma’illa Uba Misilli ya fitar a ranar Litinin, gwamnan ya bayyana kisan a matsayin zagon kasa ga zaman lafiya da tsaron Jihar Gombe.

“Wannan kisan Fasto Rabaren Bala Galadima babban abin takaici ne. Babu shakka, wannan aiki zagon ƙasa ne ga zaman lafiya da tsaro wanda Jihar Gombe ta shahara da shi.

“Ba za mu lamunci irin waɗannan abubuwa da ke kawo cikas ga zaman lafiya a jiharmu ba,” in ji Gwamna Yahaya.

Gwamnan ya kuma umurci hukumomin tsaro da su zakulo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da gurfanar da su a gaban kotu.

Ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da goyon baya ga hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa irin wannan lamari bai sake faruwa ba.

Gwamnati ta kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kasance masu kula da tsaron kansu tare da sanar da hukumomin tsaro duk wani motsi da suke zargin zai iya kawo barazana ga zaman lafiya.

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci a jihar.

A nasu ɓangaren, rundunar ’yan sandan Gombe ta bakin mai magana da yawunta, DSP Buhari Abdullahi ta ce tuni aka aike da jami’ai domin gudanar da bincike kuma nan gaba kaɗan za su fitar da jawabi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Gombe mahara ga zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar

Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.

Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.

TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.

Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.

Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.

An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.

Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.

Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura
  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji