HausaTv:
2025-04-15@23:19:58 GMT

Nijar : Majalisar Dinkin Duniya Ta Bukaci A Saki Mohamed Bazoum

Published: 11th, February 2025 GMT

Gungun aiki na Majalisar Dinkin Duniya kan tsare mutane ba bisa ka’ida ba, ya yi kira da a gaggauta sakin hambararen shugaban kasar Nijar, Mohamed Bazoum da matarsa ​​Hadiza.

Tun a watan Yulin 2023 ne ake tsare da Bazoum ​​a wani reshe na fadar shugaban kasar da ke Yamai, inda Likitansa ne kawai aka yarda ya ziyarce shi.

A cewar gungun aiki na Majalisar Dinkin Duniya kan tsare mutane ba bisa ka’ida ba, Mohamed Bazoum da matarsa ​​Hadiza ana tsare da su ba bisa ka’ida ba, wanda ya saba wa dokokin kasa da kasa.

Su ma lauyoyin Mohamed Bazoum A cikin wata sanarwa, sun tunatar da cewa tsohon shugaban da matarsa ​​”an hana su mu’amala da kasashen waje” dangi, abokai da ma lauyoyi  tun daga Oktoba 2023.

A watan Yunin da ya gabata ne Nijar ta cire kariyar Mohamed Bazoum na shugaban kasa, lamarin da ya share fagen yi masa shari’ar da har yanzu ba a sanya ranar da za a yi ta ba.

Lauyoyin Bazoum dai sun ce gwamnatin mulkin sojan kasar na amfani da shi a matsayin garkuwar dan Adam”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar

Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.

Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.

TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.

Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.

Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.

An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.

Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.

Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Sin Kasuwar Duniya Ce Kuma Dama Ce Ga Kasa Da Kasa
  • Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni
  • Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sin Da Vietnam Da Su Wanzar Da Daidaito A Tsarin Rarraba Hajoji
  • Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar
  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • A Kasar Gabon Brice Oligui Nguema Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa