HausaTv:
2025-03-25@14:30:30 GMT

Trump : Falasdinawa Ba Su Da Hakkin Komawa Gaza Idan Amurka Ta Kwace Yankin

Published: 11th, February 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa shirin korar  al’ummar Zirin Gaza zai hada da kwace ‘yancinsu na komawa kasarsu.

Trump ya fada a wata hira da tashar Fox News cewa shirin da yake yi a kan Gaza ya kunshi fitar da daukacin al’ummar yankin da kuma sake gina abin da ya kira ‘’Sake farfado da Gabas Ta Tsakiya’’

Ya kara da cewa za a iya samun wurare daban-daban har guda shida don Falasdinawa su zauna a wajen zirin Gaza.

Ya kuma ce za’a gina wa Falasdinawa gidaje masu kyau da inganci nesa da wajen da suke, saidai bai bayyana takamaiman wuri ba.

A wani labarin kuma Donald Trump ya fada a ranar Litinin din nan cewa cewa “watakila” zai daina ba da taimako ga Masar da Jordan idan ba su karbi Falasdinawa daga Gaza ba.

Kasashen biyu dai duk sun yi fatali da shirin na Trump.

Ko a ranar Litinin din masar ta yi watsi da “duk wani sulhu” da ke tauye hakkin Falasdinawa mazauna Gaza, bayan da ministan harkokin wajen kasar ya gana da takwaransa na Amurka a birnin Washington.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran da Masar sun tattauna kan rikicin da Isra’ila ta jefa yankin gabas ta tsakiya

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya yi kira ga kasashen duniya da su kawo karshen rikicin da Isra’ila ke ci gaba da haifarwa a yankin gabas ta tsakiya.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badr Abdelatty, Araghchi ya yi Allah wadai da sabbin hare-haren da Isra’ila ke kai wa zirin Gaza tare da hana kai agajin jin kai a yankin  a matsayin keta haddin yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta watan Janairu.

Ya kuma yi kira da a dauki matakin gaggawa a duniya kan yadda Isra’ila ke ci gaba da ruruta wutar rikici a yankin baki daya.

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza a ranar 7 ga Oktoba, 2023, amma ta kasa cimma manufofinta da ta ayyana kan yakin, duk da kashe Falasdinawa 50,000 galibi mata da kananan yara, tare da jikkata wasu fiye da 113,213.

Gwamnatin mamaya ta Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta amince da shirin tsagaita wuta da kungiyar gwagwarmayar Hamas a  Gaza, wadda aka fara aiki da ita a ranar 19 ga watan Janairu.

Bayan shudewar watanni biyu da fara aiwatar da yarjejeniyar, Isra’ila ta sa kafa ta yi fatali da ita, kuma ta ci gaba da kaddamar da hare-haren kisan kiyashi a kan al’ummar Gaza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • UNRWA : hana shigar da kayan agaji Gaza, ya jefa yankin cikin matsanancin hali
  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Iran da Masar sun tattauna kan rikicin da Isra’ila ta jefa yankin gabas ta tsakiya
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar