HausaTv:
2025-04-14@18:29:18 GMT

Trump : Falasdinawa Ba Su Da Hakkin Komawa Gaza Idan Amurka Ta Kwace Yankin

Published: 11th, February 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa shirin korar  al’ummar Zirin Gaza zai hada da kwace ‘yancinsu na komawa kasarsu.

Trump ya fada a wata hira da tashar Fox News cewa shirin da yake yi a kan Gaza ya kunshi fitar da daukacin al’ummar yankin da kuma sake gina abin da ya kira ‘’Sake farfado da Gabas Ta Tsakiya’’

Ya kara da cewa za a iya samun wurare daban-daban har guda shida don Falasdinawa su zauna a wajen zirin Gaza.

Ya kuma ce za’a gina wa Falasdinawa gidaje masu kyau da inganci nesa da wajen da suke, saidai bai bayyana takamaiman wuri ba.

A wani labarin kuma Donald Trump ya fada a ranar Litinin din nan cewa cewa “watakila” zai daina ba da taimako ga Masar da Jordan idan ba su karbi Falasdinawa daga Gaza ba.

Kasashen biyu dai duk sun yi fatali da shirin na Trump.

Ko a ranar Litinin din masar ta yi watsi da “duk wani sulhu” da ke tauye hakkin Falasdinawa mazauna Gaza, bayan da ministan harkokin wajen kasar ya gana da takwaransa na Amurka a birnin Washington.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar

Labaran da suke fitowa daga kasar Ukraine sun bayyana cewa, gwamnatin kasar tana son karban iko da bututun iskar gas na kasar Rasha wanda yake yammacin kasar da Turai, wanda kuma yake kai iskar gasa zuwa kasashen Turai.

An gina bututun tun zamanin tarayyar Soviet kuma kasashen biyu suna samun kudade masu yawa daga wannan bututun.

Gwamnatin kasar Amurka dai tana son ta dawo da kudaden da ta kashewa kasar Ukraine na makamai wacce ta karba a likacin shugaban Biden. Daga cikin dai Amurka ta bukaci Ukraine ta bada ma’adinanta na kimani dalar Amurka biliyon $500.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa jami’an gwanatocin kasashen Amurka da Ukraine sun tattauna wannan batun a ranar jumma’an da ta gabata, don tattauna batun irin ma’adinan da kasar Ukraine zasu bawa Amurka saboda biyan kudaden da take binta basgi. Har’ila yau Amurkawan sun gabatar da shawarar kasashen biyu su hada giwa don samun riba tare a aikin hakar Ma’adinan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci
  • Sin Za Ta Kara Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar Zuwa 125%