Kamfanin Harhaɗa Mota Na Dangote Ya Kera Peugeot 3008 GT A Kaduna
Published: 11th, February 2025 GMT
Kamfanin Dangote na Peugeot Automobiles Nigeria Limited (DPAN), wanda ke kera wa da tallata motocin Peugeot a Nijeriya, ya fara tarawa da haɗa sabuwar Peugeot 3008 GT a masana’antarsa da ke Kaduna.
Peugeot 3008 GT, mai injin 1.6-lita turbo mai ƙarfi, ya ƙara yawan jerin motocin da ake haɗawa a masana’antar DPAN, wanda ya ya ke samar da 301 sedan da Peugeot 5008 mai kujeru bakwai.
Hakanan, an samar da fasahar ABS don hana birki shanye wa, ESP don hana zamewa, da EBFD don daidaita birki bisa nauyin mota.
Motar na kuma ɗauke da fasahar Peugeot I-Cockpit, wacce ke da allon 12.3-inch mai nuna bayanai, touchscreen mai girman 8-inch, da kuma madannin tuƙi mai ayyuka da dama. Wannan ci gaba yana tabbatar da cewa DPAN na ci gaba da samar da motocin zamani masu inganci ga kasuwar Nijeriya.
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
Sanata Sunday Marshall Katung, mai wakiltar Kudancin Kaduna a Majalisar Dattawa, ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu mazauna yankin ke taimaka wa miyagu wajen aiwatar da ayyukan ta’addanci.
Da yake magana a taron manema labarai na Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Kudancin Kaduna (SKJF) a Zonkwa, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Zangon Kataf, Sanata Katung, ya jaddada cewa hukumomin tsaro na kara ɗaukar matakan daƙile matsalar a Kauru, Kachia da sauran yankunan da abin ya shafa.
Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Peter ObiYa gargaɗi duk masu bai wa ’yan ta’adda mafaka ko goyon baya da su daina, domin hukuma za ta ɗauki matakin ladabtar da su.
Sanatan ya kuma bayyana aniyarsa ta horar da matasa a fannin fasahar zamani da ICT domin su samu ƙwarewa da damar gogayya a matakin ƙasa da ƙasa.
Har ila yau, ya yaba da ƙoƙarin shugabanni da masu ruwa da tsaki wajen samar da Jami’ar Fasaha ta Tarayya da ke Kachia, wacce yanzu ke da reshe a garin Manchok.
Dangane da batun canza Asibitin Tunawa da Sir Patrick Ibrahim Yakowa da ke Kafanchan zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya, Katung, ya bayyana cewa ƙudirinsa yana jiran sauraron ra’ayoyi a Majalisar Dattawa.
Ya ƙara da cewa ƙudiri makamancinsa a Majalisar Wakilai ya riga ya kai matakin karatu na uku, kuma bayan amincewar Majalisar Dattawa, za a haɗa su don gabatar wa Shugaban Ƙasa domin ya rattaba hannu.
Bugu da ƙari, Sanatan ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da ta bai wa malaman kimiyya fifiko wajen ɗaukar sabbin malamai a makarantun sakandare domin inganta harkar ilimi.
A nasa ɓangaren, Shugaban SKJF, Ango Bally, ya ce taron manema labaran wani ɓangare ne na ƙoƙarin ƙungiyar na wayar da kan jama’a kan ayyukan Sanata Katung a Majalisar Dattawa.