Pezeshkian : Iran Za Ta Dakile Duk Makircin Makiya
Published: 11th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi kokarin dakile duk wani makirce-makircen da makiya ke kitsawa.
Shugaban na Iran ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a shekara ta 1979 a birnin Tehran yau Litinin.
Shugaba Pezeshkian Ya soki ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan na cewa yana son tattaunawa da Iran yayin da a lokaci guda ya ba da umarnin kakaba wa Iran takunkumi kan man da take fitarwa zuwa sifiri.”
Trump ya yi ikirarin cewa Iran na kawo cikas ga tsaron yankin amma “Isra’ila ce, tare da goyon bayan Amurka, tushen duk wani rashin tsaro a yankin da jefa kisan kiyashi a Gaza, hare-hare a kasashen Lebanon, Siriya, Iran da kuma duk inda ta ga dama.”
Pezeshkian ya yi gargadin cewa makiya suna neman haifar da fitina a cikin Iran, Sai dai kuma ba su san cewa a karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei da kuma irin sadaukarwar da al’ummar Iran suke yi, za’a kawo karshen duk wannan mafarki.
Shugaban na Iran ya kara da cewa, Iran ba ta taba neman kaddamar da yaki kan wata kasa ba, kuma ba za ta taba mika wuya ga makiya ba.
Iran ba za ta taba barin makiya su aiwatar da munanan manufofinsu ba, in ji shugaba Pezeshkian.
Ya nanata kudurin Iran na samun zaman lafiya tare da makwabtanta bisa ‘yan uwantaka da mutunta juna, game da batun Gaza kuma, muna kare wadanda ake zalunta ne inji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
Iran, ta yi Allah wadai da harin ta’addancin da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane a wani masallaci a kudu maso yammacin Jamhuriyar Nijar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya yi kakkausar suka kan harin da aka kai wa masallata.
Akalla mutane 44 ne suka mutu yayin da 13 suka jikkata a harin da aka kai a kauyen Fonbita da ke cikin kauyan Kokorou dake jihar Tillabery wanda ya faru a lokacin da wasu ‘yan ta’addan na kungiyar Da’ish a yankin Sahara (ISGS) suka far wa masallacin, inda suka auka wa masu ibada dake sallar Juma’a.
Baghaei ya bayyana cewa, wannan ta’addancin da aka aikata a lokacin sallar Juma’a ya saba wa ka’idar Musulunci, kuma ya saba wa dukkanin ka’idojin shari’a da hakkin dan Adam na kasa da kasa.
Kakakin na Iran ya jaddada muhimmancin kara inganta hadin gwiwa a matakai daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa don dakile da yaki da ta’addanci.
Ya zama dole a gurfanar da masu hannu a harin ta’addanci da kuma hukunta su.
Baghaei ya nuna juyayi ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su da gwamnati da kuma al’ummar Nijar kan harin ta’addanci.