Wani Sanatan Amurka Ya Taso Shugaban Kasar Tunusiya Gaba Da Tsarin Dimokaradiyyar Kasar
Published: 11th, February 2025 GMT
Wani sanatan Amurka yana barazana ga shugaban kasar Tunisiya da neman rusa nasarar dimokuradiyyar kasar
Sanatan Amurka Joe Wilson, dan majalisar wakilai daga shiyar kudancin jihar Carolina, ya kaddamar da hari kan shugaban kasar Tunusiya Qais Sa’id, inda ya dauke shi a matsayin “dan mulkin kama karya” tare da yin kira da a kakabawa Tunisiya takunkumi har sai ta dawo kan tsarin dimokiradiyya.
Maganganun Wilson, wanda ya shahara da kare matakan muggan laifukan yahudawan sahayoniyya da kuma tsantsar kiyayya ga kungiyoyin gwagwarmaya da dukkan gwamnatocin Larabawa da na Musulunci da suka ki amincewa da Shirin daidaita alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila, ya fuskanci mayar da martani mai yawa a tsakanin ‘yan siyasar Tunisiya da masu fafutuka kare hakkokin dan Adama, wadanda suka soki kalamansa, ciki har da ‘yar majalisar dokokin Tunisiya, Fatima Al-Mas’di wacce ta bukaci ya nemi afuwar al’ummar Tunusiya.
Fatima ta jaddada cewa: Shugaban kasar Tunusiya yana wakiltar al’ummar kasarsa ne tare da cikakken wakilcin jama’a.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
Shugqbqn kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen sayyed Abdulmalik Badaruddin Huthi ya bayyana cewa tura wani kataparen jirgin ruwan yaki zuwa gabas ta tsakiya wanda shugaban kasar Amurka yayi wata gazawace.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalti Alhuthi yana fadar haka yau Lahadi a wani jawabin da ya gabatar ,inda yake bayyana irin halin da ake ciki a yakin da sojojin kasarsa suke fafatawa da gwamnatin kasar Amurka. Ya kuma kara da cewa jiragen yakin ruwa na kasar Amurka sun zama matsala ga gwamnatin Amurka maimakon su taimaka mata.
Kafin haka dai gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan cewa zata aiko da jirgin ruwan yaki mai suna USS Carl Vession zuwa tekun Maliya don karfafa USS Harry Truman a yakin da take fafatawa da sojojin kasar Yemen.
Shugaban kungiyar Ansarullah ya bayyana cewa sojojin kasar Yemen zasu ci gaba da abinda suka sa a gaba na maida martini kan jiragen yakin Amurka a tekun Red Sea da kuma dukkan jiragen HKI ko wadanda suke zuwa can don tallafawa mutanen Gaza.
Shugaban kasar Amurka donal Trump dai ya sha alwashin shefe kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen daga Doron kasa.