Abin Kunya Ne Nijeriya Har Yanzu Ba Ta Iya Ciyar Da Kanta – Gwamna Bala.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.

Gwamnatin jihar Jigawa ta bada kwangilar sanya kwalta akan hanyar Dolen kwana zuwa Garin Gabas zuwa Hadejia, kan naira miliyan dubu bakwai da miliyan dari takwas.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a wajen bikin kaddamar da aikin sanya kwaltar.

Ya ce aikin hanyar mai tsawon kilomita 29, ana sa ran kammalawa nan da watanni 12 masu zuwa.

Malam Umar Namadi ya kara da cewar, an bada aikin sanya kwaltar ne da kuma sauran ayyukan inganta hanyoyi domin saukakawa manoma da sauran al’umma harkokin sufuri.

A don haka, ya yi kira ga al’ummar jihar da su rinka sa ido akan kayayyakin da hukuma ta samar musu domin gudun lalacewa da kuma barnatarwa.

A jawabinsa na maraba, kwamishinan ayyuka na Jihar, Injiniya Gambo S Malam ya ce gwamnatin jihar, ta bada ayyukan hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, bikin ya samu halartar Ministar ma’aikatar Ilmi Dr. Suwaiba Ahmed Babura da Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori da kakakin majalissar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da manyan jami’an gwamnatin jihar.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma