Aminiya:
2025-03-24@23:52:24 GMT

Dalibai 179 sun kammala Digiri da Daraja ta Ɗaya a Jami’ar Bayero

Published: 11th, February 2025 GMT

Dalibai 179 za su samu shaidar Digiri Mai Daraja ta Ɗaya a yayin bikin yaye ɗalibai na Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).

Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Abba, ya bayyana cewa dalibai 4,402 ne za a yi bikin yaye su a ranar farkon, inda a za a ba su shaidar kammala Digirin farko da Difloma da sauran makamantansu.

Bikin yaye ɗaliban shi ne karo na 39 da za a gudanar a jami’ar ta BUK.

Bikin na kwana huɗu ya kunshi jawabai da laccoci da taruka da kuma bayar da kyaututtuka da takardun shaida a matakai daban-daban.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Matan Arewa Karantar Ilimin Kimiyya?

Farfesa Sagir Abbas ya bayyana cewa a rana ta biyu za a yaye ɗalibai 4,367 daga tsangayu bakwai.

Daga cikinsu mutum 275 za su samu shaidar Digiri na Uku (PhD), 2,590 kuma masu Digiri na Biyu, sai musu 535 masu Diflomar Gaba da Digiri (PGD).

Akwai kuma waɗanda za a ba wa Digirin Girmamawa (Honoris Causa) da kuma Farfesan Ferfesoshi (Emiritus).

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai

এছাড়াও পড়ুন:

Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran

Kasar Rasha ta bayyana cewa dole Moscow da Beijing su shiga shawarwarin tattaunawar nukiliya da Iran.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta bayyana cewa, Moscow a shirye take ta samar da ingantacciyar hadin gwiwa da dukkan bangarorin kan batun yarjejeniyar nukiliyar Iran. “

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa ya aike da wasika zuwa Tehran domin fara tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran; yayin da shi da kansa ya fice daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a wa’adinsa na farko.

A halin da ake ciki dai ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.

Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) ranar Alhamis.

Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.

Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”

Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.

A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • Fiye Da Dalibai 4,200 Suka Amfana Da Tallafin Ilimi Na Sanata Solomon Adeola
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Masarautar Bauchi Ta Sauya Shawara: Za A Yi Hawan Daushe