An nada sabon Mataimakin Mai Tsawatarwa na Majalisar Tarayya
Published: 11th, February 2025 GMT
Honorbaul Isika Ibrahim ya zama sabon Mataimakin Mai Tsawatarwa na Majalisar Wakilai.
Majalisar Tarayya ta nada shi ne bayan rasuwar Honorabul Oriyomi Onanuga, mai rike da mukamin.
Shugaban Majalisar, Honorabul Tajuddeen Abbas ne ya sanar da haka a yayin zaman majaliasr a safiyar Talata.
A watan Janairu ne Allah Ya yi wa Onanuga rasuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Majlaisar Tarayya Mataimakin Mai Tsawatarwa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Barri ya jaddada cewa; HKI tana kokarin jefa Lebanon cikin tarkon kulla alaka da ita, yana mai jaddada cewa; Ko kadan Lebanon ba ta kama wannan hanyar ba.
Nabih Barri ya bayyana yadda wasu rahotanni daban-daban suke Magana akan cewa Amurka tana kai gwauro da mari, domin ganin an bude alaka kai tsaye a tsakanin Lebanon da HKI.
Shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya ce, ko kadan kasar Lebanon ba ta tunanin kulla alaka da HKI.
Haka nan kuma ya yi ishara da tsagaita wutar yaki wacce a kodayaushe HKI take ketawa, yana mai tabbatar da cewa Hizbullah tana riko da ita, don haka ya yi kira ga Amurka da sauran bangarorin da suke a cikin tsagaita wutar da su yi matsin lamba ga HKI domin ta yi aiki da ita.
Bugu da kari Nabih Barri ya ce; Sojojin kasar ta Lebanon sun gama shiryawa domin shiga cikin kudancin tafkin Laitani, amma matsalar da ake fuskanta ita ce yadda Isra’ila take kin janyewa daga wasu yankuna a cikin Lebanon.
Nabih Barri ya kuma jaddada cewa; Kungiyar Hizbullah tana aiki da tsagaita wutar yakin, kuma ba ta keta ta ba ko kadan.
Shugaban Majalisar Dokokin kasar ta Lebanon ya kara da cewa; Duk da cewa HKI tana keta tsagaita wutar yaki, amma ko sau daya Hizbullah ba ta harba ko harsashi daya ba.