Gwamnatin Jigawa Za Ta Kara Habbaka Noman Dabino A Jihar
Published: 11th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta kara jaddada kudurinta na yin hadin gwiwa da wani kamfanin sarrafa dabino da kayan marmari domin inganta noman dabino da alkama a jihar.
Gwamna Umar Namadi ya bada wannan tabbaci a lokacin da tawagar Babban Daraktan kamfanin, Dakta Abubakar Musa Bamai ta ziyarci shi a gidan Gwamnati dake Dutse, Babban Birnin Jihar.
Ya bayyana cewar, Gwamnatin a shirye take ta yi aiki tare da kowace kungiya da ke da niyyar tallafa wa jin daɗin al’umma da ci gaban tattalin arzikin jihar jigawa.
Malam Umar Namadi ya kara da cewar a zancen ma dai da ake yi a halin yanzu, Jihar Jigawa ta shahara wajen noman dabino kuma ita ce ta daya a noman alkama a ƙasar nan.
Kazalika, yayi nuni da cewar ana shirin amfani da fasahar zamani domin habaka harkar noma don ci gaba da riƙe wannan matsayi.
Tunda farko a jawabinsa, Babban Daraktan kamfanin, Dakta Abubakar Musa Bamai, ya bayyana cewar sun kai ziyarar ce domin tattauna hanyoyin hadin gwiwa da Gwamnatin Jihar Jigawa wajen kafa gonakin dabino da inganta noman alkama ta amfani da fasahar zamani.
Namadi, ya ce gonakin za su kunshi nau’uka hudu na dabino da za su bai wa jihar damar fara fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje maimakon amfani da su a cikin gida kawai.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
A ci gaba da shimfida ikonsu da suke yi a cikin birnin Khartum, sojojin Sudan sun kwace iko da babban bankin kasar, kwana daya bayan da su ka kori dakarun kai daukin gaggawa daga fadar shugaban kasa.
Kamfanin dillancin labarun “Reuters” ya nakalto majiyar sojojin Sudan tana cewa; A yau Asabar sun yi nasarar kwace iko da babban bankin kasar, tare kuma da shimfida ikonsu a cikin wasu yankunan na birnin Khartum.
Kakakin sojan kasar Sudan Nabil Abdullah, ya bayyana cewa; Mun rusa sojoji da kayan aikin abokan gaba. Haka nan kuma Abdullah ya sanar da kwace wasu ma’aikatu da suke a tsakiyar birnin Beirut da su ka kasace a karkashin ikon dakarun kai daukin gaggawa.
Ana zargin rundunar kai daukin gaggawa da tafka laifukan yaki a cikin yankunan da a baya su ka shimfida ikonsu a ciki, har da babban birnin kasar Khartum.