Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-14@17:37:29 GMT

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kara Habbaka Noman Dabino A Jihar

Published: 11th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kara Habbaka Noman Dabino A Jihar

Gwamnatin Jihar Jigawa ta kara jaddada kudurinta na yin hadin gwiwa da wani kamfanin sarrafa dabino da kayan marmari domin inganta noman dabino da alkama a jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bada wannan tabbaci a lokacin da tawagar Babban Daraktan kamfanin, Dakta Abubakar Musa Bamai ta ziyarci shi a gidan Gwamnati dake Dutse, Babban Birnin Jihar.

Ya bayyana cewar, Gwamnatin a shirye take ta yi aiki tare da kowace kungiya da ke da niyyar tallafa wa jin daɗin al’umma da ci gaban tattalin arzikin jihar jigawa.

Malam Umar Namadi ya kara da cewar a zancen ma dai da ake yi a halin yanzu, Jihar Jigawa ta shahara wajen noman dabino kuma ita ce ta daya a noman alkama a ƙasar nan.

 

Kazalika, yayi nuni da cewar ana shirin amfani da fasahar zamani domin habaka harkar noma don ci gaba da riƙe wannan matsayi.

Tunda farko a jawabinsa, Babban Daraktan kamfanin, Dakta Abubakar Musa Bamai, ya bayyana cewar sun kai ziyarar ce domin tattauna hanyoyin hadin gwiwa da Gwamnatin Jihar Jigawa wajen kafa gonakin dabino da inganta noman alkama ta amfani da fasahar zamani.

Namadi, ya ce gonakin za su kunshi nau’uka hudu na dabino da za su bai wa jihar damar fara fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje maimakon amfani da su a cikin gida kawai.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

A wannan Litinin ɗin ce ne aka rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Jihar Katsina waɗanda aka gudanar da zaɓensu a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.

Babban Jojin Jihar Katsina, Mai Shari’a Musa Danladi Abubakar ne ya jagoranci rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomin.

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato

Sai dai gab da lokacin da za a rantsar da su, ɗaya daga cikinsu ya faɗi ya sume a lokacin da yake ƙoƙarin shiga rumfar da aka tanadar masu.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bakori Honarabil Aminu Ɗan Hamidu shi ne wanda ya faɗi kuma aka ɗauka ranga-ranga zuwa asibiti.

Binciken da muka yi ya nuna cewa, shugaban ya take wani sashe na babbar rigar shi ne ba tare da ya yi la’akari ba yayin da ya yunƙura da ƙarfi don hawa matattakalar shiga rumfar, lamarin da ya janyo rigar ta shaƙe shi ya faɗi a sume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)