Sin Za Ta Ci Gaba Da Tallafa Wa Kokarin Afirka Na Samar Da Wutar Lantarki Mai Tsabta
Published: 11th, February 2025 GMT
An ce, tsakanin shekarar 2000 zuwa 2023, kasar Sin ta samar da rance da yawansa ya kai kimanin dalar Amurka biliyan 43 ga kasashen Afirka, don su raya bangaren samar da wutar lantarki. Kana a shekarun nan, kamfanonin kasar Sin sun gudanar da dimbin ayyukan samar da wutar lantarki a nahiyar Afirka, kamarsu madatsar ruwa ta Souapiti ta kasar Guinea, da madatsar ruwa ta Djibloho dake kasar Guinea Bissau, da dai sauransu.
Na biyu shi ne, fasahohin Sin a fannin zamanantarwar bangaren samar da wutar latarki suna da amfani ga kasashen Afirka a kokarinsu na raya kasa.
Kasar Sin ta kafa tsarin samar da wutar lantarki mai tsabta mafi girma a duniya, inda fitattun fasahohi da ta samu suka zamo masu rahusa kuma suka dace da yanayin da kasashen Afirka ke ciki. Kana kamfanonin kasar da suke taka muhimmiyar rawa a duniya a fannin sauya salon samar da makamashi mai tsabta, su ma za su iya taimaka wa kasashen Afirka kafa masana’antun hada injunan samar da wutar lantarki.
Na uku shi ne, Sin da Afirka sun cimma matsaya daya a fannin zamanantar da kasa ta hanya mai tsabta. A wajen taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bara, Sin da Afirka sun daddale yarjeniyoyi a bangarorin kara yin amfani da makamashi da ake sabuntawa a Afirka, da karfafa hadin gwiwar bangarorin samar da sabbin makamashi, da kara kaimi ga zamanantarwar tsarin kula da aikin makamashi na Afirka, da dai sauransu, wadanda suka nuna ra’ayi daya da kasashen Afirka da Sin suka samu a fannin manufar raya kasa. Hakan ya zo daidai da maganar da Cliff Mboya, masani dake aiki a cibiyar nazarin huldar Afirka da Sin ta kasar Ghana, ya fada, wato “Kasar Sin na kokarin daidaita manufofinta don neman dacewa da Ajandar shekarar 2063 da kungiyar kasashen Afirka AU ta gabatar”. (Bello Wang)
কীওয়ার্ড: samar da wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta kafa runduna ta musamman a kasar don magance matsalolin tsaro daban-daban wadanda kasar take fama das u.
Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto ministan tsaron kasar Muhammad Badaru yana fadar haka a lokacinda yake kaddar da wani bangaren na rundunar a barikin Kabala da ke barikin Jaje a kusa da birnin Kaduna daga arewacin kasar a jiya Litinin.
Badaru ya kara da cewa gwamnatin kasar tag a akwai butara da samar da irin wannan rundunar, saboda magance matsalolin tsaro daban-daban wadanda aka dade ana fama das u, ko kuma wadanda suke tasowa nan da ca.
Ya kara da cewa rundunar da aka kaddamar a jiya litinin bangare ne na runduna mai sojoji 800 da za’a samar saboda wannan gagarumin aikin tabbatar da tsaro a kasar. Idan an kammala hurasda sojojin zasu zama abin dogaro a lokacinda ake bukatar daukin gaggawa a ko ina a kasar.