Sin Za Ta Ci Gaba Da Tallafa Wa Kokarin Afirka Na Samar Da Wutar Lantarki Mai Tsabta
Published: 11th, February 2025 GMT
An ce, tsakanin shekarar 2000 zuwa 2023, kasar Sin ta samar da rance da yawansa ya kai kimanin dalar Amurka biliyan 43 ga kasashen Afirka, don su raya bangaren samar da wutar lantarki. Kana a shekarun nan, kamfanonin kasar Sin sun gudanar da dimbin ayyukan samar da wutar lantarki a nahiyar Afirka, kamarsu madatsar ruwa ta Souapiti ta kasar Guinea, da madatsar ruwa ta Djibloho dake kasar Guinea Bissau, da dai sauransu.
Na biyu shi ne, fasahohin Sin a fannin zamanantarwar bangaren samar da wutar latarki suna da amfani ga kasashen Afirka a kokarinsu na raya kasa.
Kasar Sin ta kafa tsarin samar da wutar lantarki mai tsabta mafi girma a duniya, inda fitattun fasahohi da ta samu suka zamo masu rahusa kuma suka dace da yanayin da kasashen Afirka ke ciki. Kana kamfanonin kasar da suke taka muhimmiyar rawa a duniya a fannin sauya salon samar da makamashi mai tsabta, su ma za su iya taimaka wa kasashen Afirka kafa masana’antun hada injunan samar da wutar lantarki.
Na uku shi ne, Sin da Afirka sun cimma matsaya daya a fannin zamanantar da kasa ta hanya mai tsabta. A wajen taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bara, Sin da Afirka sun daddale yarjeniyoyi a bangarorin kara yin amfani da makamashi da ake sabuntawa a Afirka, da karfafa hadin gwiwar bangarorin samar da sabbin makamashi, da kara kaimi ga zamanantarwar tsarin kula da aikin makamashi na Afirka, da dai sauransu, wadanda suka nuna ra’ayi daya da kasashen Afirka da Sin suka samu a fannin manufar raya kasa. Hakan ya zo daidai da maganar da Cliff Mboya, masani dake aiki a cibiyar nazarin huldar Afirka da Sin ta kasar Ghana, ya fada, wato “Kasar Sin na kokarin daidaita manufofinta don neman dacewa da Ajandar shekarar 2063 da kungiyar kasashen Afirka AU ta gabatar”. (Bello Wang)
কীওয়ার্ড: samar da wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Siyasar Kasar Iran Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah sayyid Ali Khamnei wanda ya gana da sarkin Katar a jiya Laraba ya bayyana cewa; Siyasar Iran ta ginu ne akan kyautata alaka da kasashen makwabta, kuma tuni an cimma sabbin matakai a wannan fagen.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma fada wa sarkin na Katar Tamim Bin Hamad ali-Sani cewa, ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci yana fadi tashi a wannan fagen na kyautata alaka da kasashen makwabta, tare da yin kira da cewa yarjeniyoyin da aka kulla su zama masu kare maslahar kasashen biyu.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana kasar Katar a matsayin kasa abokiya, kuma ‘yar’uwa ta Iran, duk da cewa har yanzu da akwai wasu batutuwa da ba a kai ga warware sub a,kamar dawo da kudaden Iran da aka zuba a Bankunan kasar daga Korea Ta Kudu.
A nashi gefen sarkin Katar ya jinjinawa matakan da Iran din take dauka na taimakawa raunana a duniya, da kuma al’ummar Falasdinu, kuma yadda ta kasance a tare da Falasdinawa wani abu ne da ba za taba mancewa da shi ba har abada.