Aminiya:
2025-04-14@17:44:37 GMT

‘Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya’

Published: 11th, February 2025 GMT

Nijeriya ta zama ƙasa ta 140 a cikin jerin ƙasashen da aka fi tafka cin hanci da rashawa a duniya a shekarar 2024 a cewar ƙungiyar Transparency International.

A cikin rahoton wanda ta fitar a yau, Transparency ta ce Denmark ce ƙasar da ta kasance wadda ba ta fuskantar matsalar ta cin hanci da rashawa.

BUA ya raba wa asibitoci magunguna a Sakkwato Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya suya sheka daga PDP zuwa APC

Alƙaluman ƙasashe mafi cin hanci da rashawa a duniya ya nuna yadda Nijeriya ta koma matsayin ta 140 daga ta 145 da take a baya a sahun ƙasashe 180 mafiya cin hanci da rashawa a duniya

Rahoton wanda ya yi nazari kan ƙasashen ya yi amfani da masana da ’yan kasuwa wajen tantance matsayin kowace ƙasa.

Ma’aunin tantance munin cin hancin ya kama ne daga maki sifili zuwa 100, inda sifili ke nufin mummunan matsalar cin hanci yayin da 100 ke nufin rashin matsalar baki ɗaya.

Rahoton ya yi la’akari ne da ƙarfin hukumomi a ƙasashen, da inganci zaɓe da kuma ɗabi’ar gwamnati.

Transparency International ta ce Nijeriya tare da wasu ƙasashe kamar Uganda, Mexico, Madagascar, Iraq da Kamaru sun samu maki 26 ne cikin 100.

Sudan ta Kudu da Somaliya da kuma Venezuela na cikin ƙasashen da aka fi tafka rashawa a duniya.

Transparency ta ce cin hanci babban barazana ce ga sauyin yanayi. Ta ce hakan yana kawo cikas wajen batun rage fitar da gurɓataccen iska da masana’antu ke yi.

Shugaban ƙungiyar François Valérian ya bayyana cin hanci da rashawa a matsayin mummunar matsala mai haɗarin gaske ga duniya.

Ya ce, duk da cewa wasu ƙasashe sun yi hoɓɓasa wajen murmurewa daga matsalolin na cin hanci da Rashawa amma har yanzu wasu na cigaba da ganin ta’azzarar matsalar.

Ƙungiyar ta ce daga shekarar 2012 akwai ƙasashe 32 cikin 180 da suka yi ƙoƙarin rage matsalar ta cin hanci da rashawa kodayake 148 daga ciki ko dai suna inda suke ko kuma matsalar ta ta’azzara.

Transparency International ta ce har yanzu ƙasashe 43 basu sauya daga matakin da suke tsawon shekaru ba.

A cewar ƙungiyar, akwai biliyoyin mutane da ke rayuwa a ƙasashen da rashawa ke ci gaba da illata rayukan jama’a a wani yanayi da take haƙƙin ɗan adam ke kaiwa ƙololuwa a irin ƙasashen.

François Valérian ya buƙaci ƙasashe su miƙe tsaye wajen yaƙar matsalar ta rashawa wadda ya ce babbar barazana ce ga ci gaban demokraɗiyya da taɓarɓarewar tsaro baya ga ta’azzara take haƙƙin ɗan adam.

A shekarar 2019 Nijeriya ta koma ta 146 bayan samun maki 26 yayinda ta koma ta 154 a 2021 bayan samun maki 24, inda ta koma ta 145 a 2023 bayan samun maki 25 gabanin komawa ta 140 a bana bayan samun maki 26.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: rashawa Transparency International cin hanci da rashawa a rashawa a duniya bayan samun maki Nijeriya ta matsalar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce shirye-shirye sun yi nisa game da aikin Hajjin shekarar 2025 a jihar.

Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga Radio Nigeria a hedikwatar hukumar da ke Dutse.

A cewarsa, zuwa yanzu hukumar ta mika sunayen maniyyata fiye da dubu ɗaya da suka kammala biyan kuɗin aikin Hajji daga jihar zuwa ga Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON).

Ya ce tuni aka fara shigar da waɗanda suka kammala biyan kuɗin cikin tsarin neman biza.

Labbo ya bayyana cewa hukumar ta biya Hukumar Hajji ta Ƙasa kuɗi naira biliyan takwas a madadin  alhazan jihar na shekarar 2025.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce ana gudanar da tarukan bita ga maniyyata a kullum, a kananan hukumomi 27 na jihar, ta hannun wasu malamai don ilmantar da su game da aikin hajjin.

Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba jakunkuna da za su daukin nauyin  kilo 8 da unifom ga jami’an yankuna da cibiyoyi domin rabawa mahajjatan.

Shugaban hukumar ya ja hankalin maniyyatan da su riƙa halartar traon bita saboda muhimmancinsa.

Ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake ba hukumar domin samun nasarar gudanar da aikin hajji ba tare da wata tangarda ba.

Radio Nigeria ta ruwaito cewa Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ware kujeru sama da 1,800 ga jihar domin aikin hajjin bana.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu