Aminiya:
2025-02-22@06:31:05 GMT

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

Published: 11th, February 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta bayyana aniyarta na kafa Hukumar Kula da Masu Buƙata ta Musamman a wani mataki na tabbatar da adalci a tsakanin al’ummar jihar.

Kwamishiniyar Mata da Yara masu bukata ta musamman, wacce Daraktar Jin Daɗi ta ma’aikatar, Binta Muhammad Yakasai, ta wakilta, ta bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa na yini guda da masu ruwa da tsaki kan kafa Hukumar Kula da Mutanen da ke da Bukatu na Musamman (PWDs) a Jihar Kano.

Tana jaddada aniyar gwamnati na ƙarfafa PWDs, Yakasai ta ce, “Wannan taro ba kawai haɗuwar ra’ayoyi ba ne, amma wani mataki ne na tabbatar da adalci, haɗawa da ƙarfafa wani muhimmin ɓangare na al’ummarmu.”

Ta bayyana manyan dalilai guda biyar da ke nuna bukatar kafa hukumar PWDs a Kano, waɗanda suka haɗa da kare Haƙƙoƙin PWDs – hukumar za ta kasance mai sa ido don tabbatar da an kiyaye haƙƙoƙinsu da kuma magance wariya.

Sauran sun hada da kirkira da aiwatar da tsare-tsare, inganta samun sauƙin shige da fice, karfafawa da gina kwarewa da haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki.

Yayin da tattaunawa ke ci gaba, masu ruwa da tsaki sun buƙaci a daina tsaya kan dokoki da manufofi kawai, a mayar da hankali kan tasirin su ga rayuwar jama’a.

“Wannan ba kyauta ba ce, buƙata ce. Kafa wannan hukuma al’amari ne na adalci, mutunci, da daidaiton haƙƙi. Mu haɗa kai don ganin ta tabbata,” in ji Yakasai.

Wannan taro, wanda Giving Promise, ƙwararre a shugabanci da haɗin gwiwar matasa a VSO Nigeria, ya shirya, ya bayar da damar tattaunawa kan gaggawar buƙatar samar da hukuma da za ta kula da matsalolin da PWDs ke fuskanta.

Promise ya jaddada muhimmancin hukumar wajen tabbatar da tsare-tsare da suka dace da PWDs a Kano.

“Gwamnati dole ta haɗa kowa a ci gaban jiharmu. Barin PWDs a baya yana hana cigaba. Manufofin SDGs (Sustainable Development Goals) sun jaddada buƙatar kada a bar kowa a baya, kuma kafa wannan hukuma wani mataki ne na tabbatar da cewa PWDs ba wai kawai an haɗa su ba, har ma suna da tasiri a cikin manufofin da suka shafe su,” in ji shi.

Ya bayyana manyan matsalolin PWDs guda biyu da suka haɗa da ƙarancin damar shiga da buƙatar tsarin haɗin gwiwa na musamman.

Ya ce kowane rukuni na PWDs yana da bukatunsa na musamman, kuma ba tare da hukuma ba, za su ci gaba da fuskantar ƙalubale.

“Idan har Kano na son ci gaba, dole a bai wa kowane ɗan ƙasa dama don bayar da gudunmawa. Kafa wannan hukuma ba kawai buƙata ba ce, wajibi ne,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Kula da Masu Buƙata ta Musamman Jihar Kano kafa hukumar tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina

Hukumar Hisbah ta rufe gidajen rawa da ke gudanar da harkokinsu a Jihar Katsina.

Hukumar ta umarci ɗaukacin masu gidajen rawa da ke gudanar da harkokinsu a cikin dare a faɗin jihar da su rufe.

Shugaban Hukumar, Dakta Aminu Usman ne ya bada umarnin tare da gargaɗin masu wuraren da matakin ya shafa.

Ya bayyana cewa ɗaukar matakin ya zama dole domin kare tarbiyya da dokokin addinin Islama da kuma barazanar tsaro a jihar.

Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano

Sanarwar da ya fitar ranar Laraba ta bayyana cewa tabbatar da tarbiyya da kare dokokin Musulunci sun zama wajibi.

Ya ci gaba da cewa, “za a ɗauki tsattsauran mataki kan duk masu kunne ƙashi, kuma ann riga an umarci jami’an tsaro da su tabbatar da bin wannan sabuwar doka.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro
  • INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta kirkiro Dokar Hana ‘Yan Siyasa Zuwa Rumfunan Zabe Da Maƙudan Kuɗaɗe
  • UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
  • Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Amince da  Kashe Naira Biliyan 33.4 Don Ayyukan Ci Gaba
  • Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Sin Ta Tabbatar Da Goyon Bayanta Ga Kafa Kasashe Biyu Ga Isra’ila Da Palasdinu
  • Gwamnatin Kano Ta Amince Da Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Tsaftar Muhalli 2,369