HausaTv:
2025-04-14@18:19:36 GMT

Kasashen Saudiyya Da Iran Sun Ki Amincewa Da Shirin Korar Falasdinawa Daga  Kasarsu

Published: 11th, February 2025 GMT

Da marecen jiya Litinin ne aka yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakin ministocin harkokin wajen Iran da na Saudiyya akan shirin Donald Trump na korar Falsdinawa daga Gaza,inda kasashen biyu su ka ki amincewa da shi.

Ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci, da takwaransa na Saudiyya Faysal Bin Farhaan, sun nuna kin amincewarsu da shirin na shugaban kasar Amurka akan mutanen Gaza.

Ministan harkokin wajen Saudiyya Faysal Bin Farhan ya ce, Saudiyya tana da matsaya tabbatacciya da ita ce kin amincewa da duk wani shiri na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza zuwa wata kasa.”

Ministan na Saudiyya ya nuna goyon bayansa ga kiran da Iran ta yi na yin taron kungiyar kasashen musulmi domin tattaunawa wannan batu.

A nashi gefen ministan harkokin wajen Iran ya ce; Shirin na Donald Trump na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza, ci gaba ne na tsohon shirin ‘yan mulkin mallaka na shafe hakkokin Falasdianwa, tare da yin kira da a dauki matakin fuskantar wannan makarkashiya.

Haka nan kuma minstan harkokin wajen na Iran ya yi tir da furucin Benjemin Netanyahu dake cewa a kafa kasar Falasdinu a cikin Saudiyya, tare da cewa wannan Magana ce ta dagawa da girman kai na ‘yan mamaya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?

Lamarin ya faru ne a lokacin da matashin mawakin yake kan dandamali ya na rera daya daya daga cikin fitattun wakokinsa, har zuwa lokacin wannan rahoto, Bilal Billa bai fitar da wata sanarwa a kafafen sadarwar ba, amma kuma faruwar lamarin ya janyo cece kuce inda wasu a bangare guda ke ganin abin da aka yi wa mawakan ya yi daidai yayin da wasu kuma ke ganin hakan bai dace ba.

Wasu na ganin cewar kalmar nan ta bahaushe da ya ce “Bokan Gida Bai Ci”, shi ne ke faruwa a kan wadannan mawakan, wasu kuma na ganin wannan wata hanya ce da aka dauko domin dakile tauraruwarsu da ke haskawa, wasu kuma ke cewa wannan kawai wata hanyar nuna hassada ce da mutanen arewacin Nijeriya ke amfani da ita saboda a kudancin kasar irin wannan ba kasafai yake faruwa tsakanin mawaka da sauran al’umma ba.

Ko ma dai minene dalilin da ya janyo jifar mawakan, ba zai rasa nasaba da banbancin ra’ayi ba kokuma rashin jituwa a tsakanin mawaka da masu saurarensu akan wani abinda su ka taba fafi ko aikatawa a cikin wakokinsu, sau da dama mawakan siyasa na fuskantar wannan kiyayya daga masoyansu wadanda ra’ayinsu ya saba a siyasance.

A wani lokaci can baya shahararren mawakin siyasa a Nijeriya Alhaji Dauda Adamu Kahutu wanda aka fi sani da Rarara ya fuskanci kalubale daga mutane da suke da banbancin ra’ayin siyasa, har ta kai ga wasu fusatattun matasa sun farmaki ofishinsa domin nuna fushi a kan wakokin suka ko tsangwama da yake yi wa gwaninsu a siyasance.

Amma kuma ba kasafai ake samun mawakan nanaye, nishadi ko soyayya da samun tsama tsakaninsu da masoyansu ba, duba da cewar mafi yawan lokutan mawakan kan sosa masu inda yake yi masu kaikayi a fagen soyayya, amma kuma wadannan al’amura da su ka faru a wannan shekarar ya jefa tambaya a zukatan wasu da dama a kan MI YA JANYO JIFAR MAWAKA A AREWACIN NIJERIYA.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran