Tafida, ya bayyana godiyar Gwamna Nasir Idris ga Sakatarorin kan irin gudunmuwar da suka bayar ga inganta bangaren Ilimi a matakin kananan hukumomi da kuma goyon baya ga gwamnatinsa a kan jagorancin al’ummar jihar.

 

Daga karshe, Gwamnan ya gode wa Sakatarorin kan irin yadda suka sadaukar da kansu wajen kawo cigaba a bangaren Ilimi a matakin kananan hukumomi 21 na fadin jihar tare da yi musu fatan alkairi a rayuwarsu ta gaba.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.

Gwamnatin jihar Jigawa ta bada kwangilar sanya kwalta akan hanyar Dolen kwana zuwa Garin Gabas zuwa Hadejia, kan naira miliyan dubu bakwai da miliyan dari takwas.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a wajen bikin kaddamar da aikin sanya kwaltar.

Ya ce aikin hanyar mai tsawon kilomita 29, ana sa ran kammalawa nan da watanni 12 masu zuwa.

Malam Umar Namadi ya kara da cewar, an bada aikin sanya kwaltar ne da kuma sauran ayyukan inganta hanyoyi domin saukakawa manoma da sauran al’umma harkokin sufuri.

A don haka, ya yi kira ga al’ummar jihar da su rinka sa ido akan kayayyakin da hukuma ta samar musu domin gudun lalacewa da kuma barnatarwa.

A jawabinsa na maraba, kwamishinan ayyuka na Jihar, Injiniya Gambo S Malam ya ce gwamnatin jihar, ta bada ayyukan hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, bikin ya samu halartar Ministar ma’aikatar Ilmi Dr. Suwaiba Ahmed Babura da Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori da kakakin majalissar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da manyan jami’an gwamnatin jihar.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara