HausaTv:
2025-04-14@18:24:37 GMT

Sharhin Bayan Labarai :Traump Yana Bawa Iran Zabi Nukliya Ko Yaki

Published: 11th, February 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka. Sharhin bayan labarammu zai yi magana ne dangane da barazanar shugaban kasar Amurka ga JMI “Ko ta yarda da ta zauna kan teburin tattaunawa da ita kan shirinta na makamashin nukliya ko kuma ya tura HKI ta fermata da yaki’. Wanda ni tahir amin zan karanta.

///… A wani lokaci a cikin jirgin saman fadar shugaban kasa shugaban kasar Amurka Donal Trump ya fadawa kamfanin dillancin labaran “NewYork Post’ dangane da shirin nukliyar kasar Iran, kan cewa ya fi son ya zauna da Iraniyawa su tattauna kan shirinta na makamashin nukliya, su yarda su dakatarda duk wani abu da ya shafi nukliya, amma idan sun ki tattaunawa, kuma bai da zabi in banda ta fermata da yaki.

A maganarsa dai shugaban yana son nuna diblomasiyya da kuma lallashi ne ga kasar Amurka ta amince da yarjeniya wacce zata daina mu’amala da sinadarin Uranium kwata-kwata, a sannan zata zauna lafiya da Amurka, amma kuma ra rusa diblomasiyyarsa da, kara takuarawa Iran da sabbin takunkuman tattalin arziki, da kuma baranar kara wasu takunkuman tattalin arziki, ko kuma idan duk wadannan sun kasa shawo kan iran ta zai bude wuta a kan cibiyoyin nukliyar kasar ta Iran ne.

Wannan matsayin da shugaban kasar Iran ya bayyana ba matsayi ne na diblomasiyya ba, sai dai barazana ce, na cewa JMI bata da zabi inda banda wanda Amurka ta bada, wato ko ki yarda ki tadakar da shirin na nukliya kwata-kwata!, ki daina mu’amala da makashin nukliya, ko kuma mu farmaki da yaki. Dole ne ta zama daya daga cikin zabin da Amurka ta bata.

Sai dai bayan wannan furushin na shugaba Trump. Iran ta shigar da korafin a gaban kwamitin tsaro na MDD. Inda mataimakin ministan harkokin wajen kasar kan al-amuran sharia da kuma kasa da kasa, Kazem Gharibabadi , ya bada sanarwan cewa JMI zata shigar da korafi a gaban kwamitin tsaro na MDD. Kan cewa gwamnatin Amurka ta yi barazanar fermata da yaki.

Yaze wannan barazanar ta sabawa dokokin kasa da kasa, wace ta bawa ko wace kasa yencin kai da kuma zabin abubuwan da zata yi da wadanda basa son yin.

Shugaban Trump dai ya dade yana wannan barazanar kafin ya shiga fadar white house karo na biyu, sannan wannan ba shine karon farko da yake wannan barazanar ba. Sai dai a wannan karon ya fito karara ya bayyana shi.

Kafin haka dai su jami’an gwamnatin JMI sun yi ta sabani a tsakaninsu kan ya zauna da Amurka ne don a zauna lafiya da ita ko kuma me za’a yi?.

Amma a makon da ya gabata wato a ranar larabann da ta gabata Jagoran juyin juya halin musulinci na kasar Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya fito fili ya bayyana matsayin JMI kan wannan al-amarin wanda kuma shi ne, Iran ba zata shiga tattauna da da Amurka tare da dalilai, kwarara.

Na farko shi wannan Trump din shi ne ya fidda Amurka daga yarjenioyar JCPOA tsakanin Iran da manya manyan kasashen duniya shida. Bayan tattaunawa na shekaru kimani 2. Sannan sauran suka saba wa alkawalin da suka dawkawwa Iran a JCPOA.

Wani tattanawa kuma za’a yi da shi. Bayan da takunkuman tattalin arzikinsa suna dabaibaye da kasar Iran. Don haka ya kammala da cewa mai hankali, da kuma wanda yake son mutuncinsa, har ‘iala yau wanda baya son daukar kaskasci ba zai amince da hakan ba, Don haka Iran ba zata yi tattaunawa da wani da cikin wadannan kasashen yamma ba.

Wannan ya sa dukkan mutanen kasar Iran yan siyasa da sauran mutane suka dawo kan ra’ayin jagoran.

Don haka a halin yanzu sai mu jira mu gani me Trump zai yi bayan wannan matsaya mai karfai .

Banda haka jagoram ya bayyana cewa idan Amurka ta yi barazana , zasu yi mata barazana idan ka kawowa Iramn hari zata rama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya

Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.

Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu