A ci gaba da kokarinta na samun tagomashi a fannin tattalin arziki da ci gaban jihar ta hanyar kawo sauyi a harkar noma, gwamnatin jihar Jigawa na shirin hada gwiwa da wani kamfani da ke samar da dabino  da bayar da shawarwari a harkar noma, wanda ke da ofishi a Najeriya a kasar Saudiyya domin bunkasa noman dabino a jihar.

Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a yayin da ya karbi bakuncin wata tawaga daga daya daga cikin manyan kamfanonin noma na kasar Saudiyya, wadanda suka kware a harkar noman dabino da sarrafa gonaki, karkashin jagorancin Abdul’aziz Abdurrahman Al-Awf, wadanda suka kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati dake Dutse.

Babban makasudin ziyarar ita ce tattaunawa kan dabarun hadin gwiwa da nufin bunkasa noman dabino a Jigawa, ta hanyar bunkasar fasahar noma, da musayar ra’ayoyi, da zuba jari a fannin noma.

Da yake jawabi a wajen taron, Abdul’aziz Al-Awf ya bayyana kudirin kamfaninsa na kawo sabbin dabarun noman zamani a jihar Jigawa, tare da tabbatar da samar da dabino a duk shekara maimakon noman rani, inda ya nuna cewa hadin gwiwar zai kunshi horar da manoma sosai, da karfafawa matasa gwiwa, da kuma bullo da wasu nau’o’in dabino masu kima da yawan amfanin gona a kasar Saudiyya.

“Wannan hadin gwiwa ba wai kawai zai kara yawan dabino da ake nomawa a Jigawa ba ne, har ma da inganta shi, wanda hakan zai sa jihar ta zama cibiyar noman dabino a Najeriya da Afrika,” inji shi.

Gwamna Namadi ya bayyana cikakken goyon bayan gwamnatinsa ga shirin, yana mai cewa ya yi daidai da tsarin bunkasa noma na jihar.

“Muna maraba da ku zuwa jihar Jigawa kuma mun yaba da sha’awar ku ta yin aiki da mu. A matsayinmu na gwamnati mun jajirce sosai wajen wannan hadin gwiwa domin zai amfani al’ummarmu matuka. Ziyarar ku da kuma shirye-shiryen ku na hadin gwiwa da mu kan samar da noman dabino a fadin jihar nan, tare da inganta noman alkama, sun yi dai dai da burinmu na bunkasa noma.”

Ya bayyana  Jigawa a matsayin kan gaba wajen noman alkama a Najeriya, tare da jaddada manufarsa ta fadada noman dabino a jihar.

Gwamna Namadi ya jaddada shirin gwamnatinsa na samar da duk wani abu da ake bukata domin ganin an samu nasarar aiwatar da aikin.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa hadin gwiwar zai samar da fa’ida sosai, tare da sanya Jigawa a matsayin kan gaba a masana’antar dabino ta duniya.

“Mun himmatu wajen mai da jihar Jigawa cibiyar noman dabino, ba kawai don amfanin gida ba har ma da fitar da shi zuwa kasashen waje domin bunkasa tattalin arzikin jihar. 

A yayin ziyarar, tawagar  ta Saudiyya tare da wakilan kamfanin Netay Agro-Tech sun zagaya wurare daban-daban a fadin jihar domin tantance dabino da ake da su.

Abubakar Musa Bamai, Shugaban Kamfanin Netay Agro-Tech, ya bayyana dimbin ayyukan da aka riga aka yi, wadanda suka hada da nazarin kasa da tuntubar juna da cibiyoyin bincike.

Ya sanar da cewa nau’in dabino guda hudu da ake nema, wato Mejdool (Meju), Barhi (Bari), Sukkari (Sukari), da Ajwa—an bayyana su a matsayin wadanda suka dace don noma mai inganci a Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Saudiyya wadanda suka jihar Jigawa hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya

Shugaba hukumar makashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Islami ya bada sanarwan cewa a ranar 8 ga watan Afrilu mai zuwa. Yace hukumarsa za ta kaddamar da sabbin magunguna da ta samar tare da amfani da makamashin Nukliya, a dai dai na ranar makamashin Nukliya ta kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto Islami yana fadar haka a yau Lahadi, ya kuma kara da cewa wannan ci gaban kari ne, kan ci gaban da kasar ta samu a wannan fannin, wanda kuma zai kara kyautata bangaren lafiya na kasar sannan ya zama hanyar samar da kudade ga kasar.

Shugaba hukumar makamashin nukliya ta Iran ya kara da cewa a cikin shekarar Iraniyawa wanda ya kara kadai kasar ta samar da sabbin ci gaba kimani 100 tare da amfani da makamashin nucliya, kuma tana son nan da shekara ta 2040 masana’antar makamashin nukliya ta kasar Iran zata shiga cikin masana’antun makamshin nukliya mafi girma a duniya.

Ana saran shugaba Pezeshkiyan zai halarci taron kaddamarda wadandan kayakin ci gaba da aka samu a ranar 8 ga watan Afrilu mai zuwa.

Sannan Iran ta dage kan cewa shirinta na makamashin Nukliya na zaman lafiya ne, sabanin abinda kasashen yamma musamman Amurka take zargin kasar na cewa shirin ya wuce na zaman lafiya.

Sai dai kakakin Fadar Krimlin na kasar Rasha Dmitry Medbedev ya bayyana a makon da ya gabata kan cewa shirin makamashin Nukliya na kasar Iran na zaman lafiya ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Ukraine: Tawagogin Rasha da Amurka sun kammala tattaunawa a Saudiyya
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi