HausaTv:
2025-03-25@20:16:02 GMT

Kungiyar Tarayyar Afirka Ta Ce: Sudan Ce Kasar Mafi Fama Da Matsalar Jin Kai A Duniya

Published: 12th, February 2025 GMT

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bayyana cewa: Sudan ce kasar da aka fi fama da matsalar jin kai a duniya

A zaman tattaunawa da Kungiyar Tarayyar Afirka ta gudanar ta bayyana yakin basasar Sudan a matsayin “mafi girman matsalar jin kai a duniya,” inda ta yi gargadin irin mummunar illar da yake yi kan fararen hula, musamman kananan yara masu fama da rashin abinci mai gina jiki.

Wadannan kalamai sun zo ne a yayin wani taron tattaunawa da kungiyar Tarayyar Afirka ta gudanar, inda aka yi karin haske kan rikicin da ake yi tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa, wanda ya yi sanadiyyar raba mutane kimanin miliyan 12 da matsugunan su.

Yakin dai ya kawo cikas wajen kai agajin jin kai, ya haifar da karancin abinci da kuma ta’azzara yunwa, in ji Mohamed Ibn Chambas, shugaban kwamitin Tarayyar Afirka kan Sudan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida

Ebrahim Rasool, jakadan Afirka ta Kudu da gwamnatin Trump ta kora, ya samu tarba a wannan Lahadin daga daruruwan magoya bayansa da suke rera wakoki  domin karrama shi a filin jirgin sama na Cape Town.

Jama’a sun kewaye Rasool da matarsa ​​Rosieda bayan isowarsu, yayin da ‘yan sanda suka yi musu rakiya har zuwa tashar jirgin kasa.

Da yake yiwa magoya bayansa jawabi, Rasool ya ce, Abin da ya faru yana a matsayin wulakanta ku ne ku al’ummar Afirka ta kudu, amma kuma idan kuka tsaya tsayin daka kan manufofinku na ‘yancin kai to za ku ci gaba da rayuwa a cikin mutunci da daukaka.

Ya ce ba laifi muka yi ba, ammam kuma mun dawo gida ba tare da nadama ba.

Gwamnatin Trump ta kori Rasool sakamakon kalaman da ya yi a cikin shafukan yanar gizo, wanda gwamnatin Trump ke kallon kalamansa a matsayin batunci ga Amurka.

 Korar Rasool, wanda tsohon mai fafutukar yaki da wariyar launin fata ne, ya kara dagula dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, wadanda manufofin Trump na baya-bayan nan suka kara kawo tankiya da zaman doya da manja a tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Super Eagles ta gamu da cikas a ƙoƙarin neman tikitin Gasar Kofin Duniya
  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum