Kungiyar Hamas Ta Jaddada Rashin Yiwuwar Korar Falasdinawa Daga Yankin Zirin Gaza
Published: 12th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta sha alwashin dakile shirin shugaban Amurka Trump na neman tilastawa Falasdina gudun hijira daga Zirin Gaza
Kungiyar Hamas ta lashi takobin dakile shirin shugaban Amurka Donald Trump na neman tilastawa Falasdinawa gudun hijira zuwa kasashe makwabta, tare da yin watsi da barazanar da ya yi na bude kofofin jahannama a yankin Falasdinu idan har Hamas ba ta sako fursunonin yahudawan sahayoniyyar Isra’ila kafin yammacin ranar Asabar ba.
A cikin wata sanarwa da kungiyar Hamas ta fitar ta ce, abin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kasa cimmawa ta hanyar wuce gona da iri, ba zai yi nasara ba ta hanyar aiwatar da siyasar makirci da yaudara.
Sanarwar ta ce, manyan al’ummar Gaza sun tsaya tsayin daka wajen fuskantar hare-haren bama-bamai da wuce gona da iri, kuma za su ci gaba da tsayin daka kan kasarsu tare da dakile duk wani shiri na neman tilasta musu gudun hijira daga muhallinsu zuwa wasu kasashen makwabta.
Hamas ta jaddada cewa: shirin korar al’ummar Palasdinu daga Gaza ba zai yi nasara ba, kuma zai fuskanci kalubalen Falasdinawa, Larabawa da kuma al’ummar musulmi wadanda suka yi watsi da duk wani shiri na raba Falasdinawa da muhallinsu zuwa gudun hijira.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
Jami’an tsaron Jihar Edo sun sake kama wasu mafarauta hudu daga Kano, makonni kadan bayan kisan gilla da ’yan bangar Jihar Edo suka yi wa ayarin wasu mafarauta 16 daga jihar Kano a jihar.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo, ta ce mafarautan da aka kama sun fito ne daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano, kuma suna dauke da bindigogin toka guda uku, da adduna da wukake a lokacin da aka kama su.
Kakakin ’yan sanda an jihar, CSP Moses Yamu, ya ce kanawan da aka kama mafarauta ne ba kamar yadda ake yadawa a kafofin sada zumunta cewa makiyaya ba ne.
Ya bayyana cewa jami’an kungiyar tsaro ta Jhar Edo ne suka kama mafarautan sannan suka damka su ga ’yan sanda inda ake yi musu tambayoyi a ofishin ’yan sanda da ke yankin Ikpoba Hill.
’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken TinubuYa ce an, “An kama mafarautan da suka fito daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa yankin Uvbe da ke Karamar Hukumar Orhionwon a Jihar Edo. A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike.”
Da haka Kwamishinan ’yan sandan jihar, Monday Agbonika, ya gargadi jama’ar jihar da su guji yada abin da ba gaskiya ba ne game da lamarin, domin yana iya tayar da zaune tsaye.
Idan ba a manta ba, a cikin watan Ramadan, gab Sallah Karama ne ’yan banga suka yi wa wasu mafarauta 16 daga Jihar Kano da ke hanyarsu ta komawa gida hutun sallah kisan gilla a yankin Uromi da ke jihar, lamarin da ya haifar da tayar da jijiyoyin wuya, inda har yanzu ake kokarin shawo kansa.