HausaTv:
2025-03-24@12:58:39 GMT

Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce: Za A Kashe Dala Biliya 53 Wajen Sake Gina Zirin Gaza

Published: 12th, February 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa: Sake gina Gaza na bukatar kudi sama da dala biliyan 53

Wani kiyasi na Majalisar Dinkin Duniya ya fada a ranar Talata cewa: Sake gina yankin Zirin Gaza da yakin haramtacciyar kasar Isra’ila ya lalata yana bukatar kudi sama da dala biliyan 53, ciki har da sama da dala biliyan 20 cikin shekaru uku na farko.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya rubuta a cikin wani rahoto da aka shirya bisa bukatar babban zauren Majalisar Dinkin Duniya cewa: Adadin kudaden da ake bukata don farfado da sake gina yankin a cikin gajeren lokaci, matsakaita da kuma dogon lokaci a Zirin Gaza “an kiyasta kimanin dala biliyan 53 da miliyan 142. A cikin wannan adadin, an kiyasta kudaden da ake bukata a cikin gajeren lokaci na shekaru uku na farko da kusan dala biliyan 20 da 568.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya dala biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99

Bubu da kari, abin mahimmancin shi ne, shi talakan Nijeriya zai iya gani a kas na irin wadannan shirye-shiyen da gwamnatin ke son aiwatarwa?

 

Fannin Da Gwamnatin Za Ta Zuba Kudaden:

A kasafin kudin na 2025, Gwamnatin Tarayya ta warewa bangaren tsaro Naira tiriliyan 6.11 wanda ya kai ta samar da karin kaso 88 daga cikin kasafin kudin da ta warewa fannin na Naira tiriliyan 3.25 a 2024.

Shin wannan burin na Gwamnatin zai iya cika, duba da yadda aka gaza dakile ta’addanci, ‘yan fashin daji, wanda idan ba a mayar da hankali ba, a 2025, tarihi ne zai sake mai-maita kansa.

An ware Naira tiriliyan 5.99 a cikin kasafin kudin don yin tituna, gadoji da kuma manyan ayyuka a babbar hanyar da ta tashi daga Legas zuwa Kalaba da ta Sokoto zuwa Badagry, inda aka samu karin da ya kai sama da kaso 350 sabanin Naira tirliyan 1.32 da aka ware a kasafin kudin bara.

Idan har da a gudanar da wadannan ayyukan, za su kara samar da ayyukan yi da habaka kasuwanci.

Bugu da kari, a kasafin kudin na 2025, an warewa ilimi, kiwon lafiya da bunkasa hazaka Naira biliyan 5.7 wanda ya kai kaso 161, sabanin Naira tiriliyan 2.18 da aka ware a kasafin kudi na 2024, inda fannin aikin noma ya samu Naira tiriliayan 3.73, wanda hakan ya nuna an samu kari mai yawa da ya zarta na Naira biliyan 362, inda an yin wannan karin ne, don a karya farashin kayan abinci a kasar.

 

Sai dai, shin ko wannan karin kudaden zai samar wa talakawan kasar sauki?

Amma wasu kwararu a Cibiyar Tsare-Tsare Da Bincike Kan Tattalin Arzikin Kasa (CEPR) ta yi nuni da cewa, idan har ba a wanzar da kuma kara kudi a cikin kasafin kudi hakan ba zai yi tasiri ba.

 

Kara Yawan Karbo Rancen Kudade:

Kudin ruwan da bashin da Gwamnatin ke biya ya lakume Naira tirilaya 16.3, wanda ya kai kaso 98, inda hakan ya nuna an samu karin Naira 8.25 a kasafin kudi na 2024.

Sai dai, wani babban kalubalen shi ne, yadda Nijeriya ke biyan bashin kudin ruwa na bashin da ta karbo fiye da wanda rake son kashewa a bangarorin ilimi, kiwon lafiya da samar da kayan aiki.

Gwamnatin ta yi hasahsne kudaden shiga da take son samu za su karu daga Naira tiriliyan18.32 zuwa Naira 36.35 trillion, wadanda suka kai karin kaso 123.19, musamman ta hayar tara haraji da zuba hannun jari na ketare.

Duba da yadda a arihin Nijeriya ka gaza tara kudaden shigar da ake sa ran tarawa, wasu kwararru a taron kungiyar tattalin arziki Nijeriya (NESG) sun yi garadin cewa, bai mai yuwa banen wadannan hasashen da aka yi su tabbata ba.

Kasafin kudin kasar ya rubanya a cikin shekara daya, amma duk da haka kudaden shigar kasar sun yi rauni.

Alal misali, a cikin kasafin kudin na 2025, ‘yan Majalisa sun samu karin Naira biliyan 344.85, wanda a kasafin kudi na 2024, suka samu karin Naira biliyan 197.93, inda kuma su ke son ‘yan kasar su kara jan damarar ci gaba da kula da rayuwarsu.

Bugu da kari, ‘yan Malasira Dokoki sun sun samawar da kansu karin sma da Naira biliyan 7 na kudaden sun a tafiye-tafiye, da kuma wasu dimbin kudaden da suka warewa kansu na jin dadi da na biyan kafafen ‘yada labarai.

A shirye-shiyen jin kan alumma, an ware Naira biliyan 723.68 kacal wanda aka kara kudin zuwa Naira biliyan 600, amma duk da haka, wani dan bangare kadan ne, aka kashe kan ayyukan gwamnatin.

Akwai dai dimbin buri da aka sanya a cikin kasafin kudin na 2025, wanda duk da wannan burin, cin abinci sauku a rana, na neman gagarar talakan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • MDD da EU sun yi tir da wargaza yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da Isra’ila ta yi
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun