Aminiya:
2025-04-15@23:24:42 GMT

Hajjin 2025: Ana shirya wa shugaban NAHCON maƙarƙashiya – Musa Iliyasu

Published: 12th, February 2025 GMT

Jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya tabbatar da cewa Shugabancin Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan a Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ba zai gaza ba duk da ƙoƙarin yaɗa jita-jita da wasu ke yi.

Kwankwaso, ya musanta wani rahoto da ke cewa mahajjata na iya rasa zuwa aikin Hajjin 2025, inda ya bayyan cewar wannan ƙarya ce da aka shirya don yaudarar jama’a da kuma ɓata sunan shugaban NAHCON.

An yi wa kashi 25 na matan Nijeriya kaciya Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya

Ya buƙaci jama’a, musamman maniyyatan da za su yi aikin Hajjin 2025, da su yi watsi da wannan rahoto, inda ya Farfesa Pakistan yana da ƙwarewa wajen shirya aikin Hajji.

“Muna sane da jita-jitar da ake yaɗawa cewa dubban maniyyata na iya rasa zuwa aikin Hajjjin 2025.

“Wannan ƙarya ce da ake ƙoƙarin amfani da ita don kawo cikas ga Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan,” in ji Kwankwaso.

Ya zargi ’yan adawa da ɗaukar nauyin wannan jita-jita saboda tsoron nasarar da Farfesa Pakistan zai kawo tare da sauyi a tsarin aiki. Hajji.

“Muna da masaniya cewa wasu mutane na yaɗa labarai marasa tushe don ɓata masa suna.

“Manufarsu ita ce kawo cikas ga mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, amma ba za su yi nasara ba,” a cewarsa.

Kwankwaso, ya kuma bayyana cewa NAHCON ba ta soke kowace kwangila ba, inda ya alaƙanta hakan da ƙasae Saudiyya.

Ya bayyana cewa Farfesa Pakistan yana ƙasar Saudiya don warware matsalar lokacin da aka yaɗa rahoton na ƙarya.

Ya kuma tabbatar wa maniyyata cewa za a gudanar da Hajjjin 2025 cikin nasara.

“Ina kira ga duk maniyyata da su kwantar da hankalinsu. Farfesa Pakistan ya samu wannan muƙami ne saboda cancantarsa.

“Kuma yana da ƙwarewar da za ta sa a samu nasara. Babu wani maniyyaci da aka yi wa rijista da ba zai samu damar tafiya aikin Hajji ba,” in ji shi.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shi ma ya bayyana cewa babu buƙatar mutane su shiga damuwa game da lamarin.

Ya kuma ya musanta zargin cewa kwangilar da aka bai wa wasu domin gudanar da aikin Hajjin bana na iya samu matsala.

Kwankwaso ya ƙarƙare da cewa waɗanda ke yaɗa jita-jitar suna ƙoƙarin hana gwamnati samun nasara ne, kuma a cewarsa burinsu ba zai cika ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan Maƙarƙashiya maniyyata Musa Iliyasu Kwankwanso Farfesa Pakistan

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa

Ya soki masu ra’ayin cewa dimukradiyya wani sharadi ne na ci gaba, yana mai cewa “karya ne” shi akwai wata kasa da ta ci gaba a karkashin tsarin dimukradiyya?.

Burkina24 ta nakalto cewa “Babu wata kasa da za a iya bayyanawa da ta ci gaba a dimukradiyya.

Ya ci gaba da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sadarwa, bayyanawa, da kuma fahimtar da mutane mene ne juyin juya hali.

Traore ya yi fice wajen yanke shawarar ce bayan hayewarsa a matsayin shugaban kasar da ke yammacin Afirka.

Shugaban mai shekaru 37 da haihuwa wanda ya hau karagar mulki a watan Satumban 2022 ta hanyar juyin mulkin da ya hambarar da shugaban kasar na wucin gadi Paul-Henri Damiba kwanan nan ya yi watsi da tayin Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa.

Ya bukaci kasar Musulunci da ta gwammace ta saka hannun jari a wasu muhimman ayyukan more rayuwa wadanda za su amfani al’ummarsa kai tsaye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Minista Ya Gargaɗi Jami’an Gwamnati Kan Rashin Sanin Ilimin Tantance Ingantattun Labarai
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa