Aminiya:
2025-04-14@17:49:18 GMT

Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum

Published: 12th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya jaddada buƙatar samar da manyan gonakin gudanar da noman rani domin yaki da matsalar karancin abinci a Yankin Tafkin Chadi.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin taron Gwamnonin Tafkin Chadi da aka gudanar makon da ya gabatar a garin Maiduguri fadar Jihar Borno karo na biyar, inda ya jadadda cewar, Allah SWT ya azurta wannan Yanki na Tafkin Chadi da dimbin filayen noma wanda idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, na iya ba da gudummawa sosai wajen samar da abinci a yankin har ma da yankuna makwabta.

Zulum ya bayyana muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnonin yankin da abokan haɗin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya domin kafa gonakin noman rani masu inganci.

Ya yi nuni da cewa dogaro da noman damina kadai ba zai dore ba, saboda karuwar al’ummar yankin, wanda ala tilas sai an hada da noman rani.

Zulum ya kuma jaddada bukatar yin bincike kan amfanin gona masu jure yanayi don tabbatar da isasshen abinci da wadatar abinci ga al’ummar wannan yanki.

Ya ba da shawarar cewa, shirin noman ranin zai iya tallafa wa ci gaban kiwon dabbobi, yadda za a samu wadataccen nama da kuma nono a yankin.

A cewar gwamnan, “kafa manyan gonakin noman rani na buƙatar jajircewa daga gwamnoni da abokan tarayya da gwamnatocin kasashenmu don ganin mun cim ma manufar hakan a kan lokaci, yadda al’ummomin za su amfana”, in ji shi.

Ya kuma jaddada cewa, “gabar Tafkin Chadi na samar da wadataccen ruwa, kuma ana iya haka rijiyoyi da sanya bututun tura ruwa inda ruwan ya yi ƙaranci don al’ummar wuraren su amfana.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Noman rani

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu

Ga kuma yadda ake sarrafawa:

Da farko, a zuba ruwa a tukunya a sa a wuta domin ya tafasa.

A rage wuta kadan, sannan a zuba garin alabo a hankali cikin ruwan da ke tafasa, ana juyawa da muciya ko cokali ko leda mai kauri don kada ya yi kolalla.

A ci gaba da juyawa har sai ya hade sosai kuma ya zama mai laushi.

Idan yana da kauri sosai, sai a kara dan ruwan zafi kadan wanda dama kin rage, kuma a ci gaba da juyawa har sai ya yi laushi.

A rufe shi na ‘yan mintuna kafin a sauke.

 

Sai kuma yadda ake miyar Uwedu:

Iata ma ga abubuwan da ake bukata domin hada ta:

Ganyen Ewedu (fresh leabes)

Kanwa ko potash (dan kadan),Gishiri, Magi, yaji

 

Sai kuma yadda ake hadawa:

A gyara ganyen Ewedu, a wanke su da kyau.

Sannan a zuba ruwa kadan a tukunya, a sa kanwa ko potash, a sa a tafasa.

Idan ruwan ya tafasa, sai a zuba ganyen uwedu, a dafa na kimanin minti 5–7. A sauke, sannan a daka a cikin turmi ko a murza da blender idan ana so ya zama ya yi laushi. Sai a mayar da shi tukunya, a sa gishiri da maggi da yaji idan ana so, a dafa na minti kadan sai a sauke.

A ci dadi lafiya.

Za’a dan iya zuba miyar ja ko nama ko ganda ko kifi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno