An Yi Bikin Cika Shekaru 46 Na Nasarar Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran, A Burkina Faso
Published: 12th, February 2025 GMT
Iraniyawa mazauna kasar Burkina Faso sun gudanar da bukukuwan murnar cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a birnin Ouagadougou.
A wannan karon, kasashen biyu sun daukaka kyakkyawar dangantakarsu da aka gina a shekarar 1984.
Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Ouagadougou, Mojtaba Faghihi, wanda ya halarci bikin, ya bayyana cewa juyin juya halin Musulunci a Iran a shekara ta 1979 ya ba da damar “yantar da mu daga tsoma bakin siyasa na kasashen waje da wawashe dukiyarmu”.
A cewarsa, Iran ta samu nasarar dakile makircin makiya da kuma wuce gona da iri na sojojin kasashen waje, da takunkumi da kuma ta’addanci.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Burkina Faso, Karamoko Jean-Marie Traoré, ya bayyana jin dadinsa da raba wannan lokaci karkashin alamar abota da hadin kai tsakanin al’ummomin kasashen biyu, wadanda suka yanke shawarar tafiya tare tun daga shekarar 1984.
Ya kuma mika sakon shugaban Burkina Faso Kyaftin Ibrahim Traoré, na taya murna dangane da cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci.
A cewarsa, Iran ita ma kasa ce “da za mu iya koyo daga gare ta, musamman daga juriyarta, hazaka da jaruntaka”.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
Cibiyar ta “ Global 196” ta bakin babban shugabanta ta sanar da cewa a cikin watanni 18 da su ka gabata, ta tattara bayanai akan laifukan yakin da Isra’ila ta tafka a Gaza.” Haka nan kuma cibiyar mai matsuguni a Birtaniya ta ce, ya zuwa yanzu ta tattara da dalilai da su ka dace da ka’idojin shari’a a kotunan manyan laifuka na kasar.
Har ila yau cibiyar ta ce, bayan kammala tattara bayanai a zango na farko, za kuma ta bude shafi na gaba domin kara samun wasu bayanan da za su tabbatar da cewa an yi wa Isra’ilawan hukunci a cikin kasashen duniya, musamman masu dauke da zama ‘yan kasashe biyu.
Wani shiri da wannan cibiyar take da shi,shi ne na samar da wasu cibiyoyin a cikin nahiyoyin duniya da samar da ka’idoji ta fuskar shari’a da su ka dace da na duniya da kuma na kasashe domin farautar wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza, da fitar da sammacin kamo su, saboda su fuskanci shari’a.
Wadanda wannan cibiyar take son ganin sun fuskanci shiri’a, sun hada jami’an sojan HKI, da ‘yan siyasa da duk masu hannu a aikata laifukan yaki.
Ita wannan cibiyar ta kunshi kawance na lauyoyi daga kasashen Malysia, Turkiya, Norway, Canada, Bosnia, da kuma Birtaniya.
Ana kuma sa ran cewa anan gaba wasu lauyoyin daga wasu kasashen duniya za su shiga ciki,musamman a wannan lokacin da HKI ta bude wani sabon kisan kiyashin akan al’ummar Falasdinu.
Cibiyar ta kasa da kasa mai son ganin an yi wa Falasdinawa adalci, ta kuma hada da fitaccen lauyan nan dan kasar Afirka Ta Kudu John Dugard, da kokarin jawo lauyoyi daga dukkakin kasashen duniya.
Cibiyar za ta yi aiki domin ganin a kowace jaha da gunduma ta kasashen duniya an samar da hanyar hukunta wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza.