HausaTv:
2025-04-14@18:31:47 GMT

Aljeriya Ta Yi Maraba Da Shirin Iran Na Gudanar Da Taron OIC Kan Gaza

Published: 12th, February 2025 GMT

Kasar Aljeriya ta yi marhabin da shirin Iran na gudanar da taron kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a zirin Gaza, wanda shugaban na Amurka ya ce yana son karbe iko tare da raba al’ummar kasar baki daya.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya gabatar da shawarar gudanar da wani zama na musamman na kungiyar OIC a ranar Litinin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Aljeriya Ahmed Attaf, a wani bangare na tuntubar da yake yi da ministocin harkokin wajen kasashen musulmi kan Gaza.

A yayin tattaunawar tasa, Mista Araghchi ya yi cikakken bayani kan shawarwarin da ya yi a baya-bayan nan da shugabannin kasashen musulmi, da kuma babban sakataren kungiyar OIC, Hussein Ibrahim Taha, da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, don jawo hankalin al’ummar duniya kan “makircin tsarkake kabilanci a Gaza”.

Shugaban diflomasiyyar na Iran ya yi maraba da matakin da Aljeriya ta dauka na nuna goyon baya ga tsayin daka da al’ummar Palastinu suke yi na ‘yantar da kansu daga mamayar Isra’ila.

A makon da ya gabata, Trump ya ce Amurka na neman “karbe” Gaza a wani bangare na shirin da ya gabatar a karkashin sunan “sake gina” yankin Falasdinawa da yaki ya daidaita, inda ya ba da shawarar tilastawa wasu ‘yan Gazan miliyan 2.4 gudun hijira zuwa Masar da Jordan.

Tuni dai Alkahira da Amman suka yi watsi da shirin na Trump na tunzura jama’a.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing