Aljeriya Ta Yi Maraba Da Shirin Iran Na Gudanar Da Taron OIC Kan Gaza
Published: 12th, February 2025 GMT
Kasar Aljeriya ta yi marhabin da shirin Iran na gudanar da taron kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a zirin Gaza, wanda shugaban na Amurka ya ce yana son karbe iko tare da raba al’ummar kasar baki daya.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya gabatar da shawarar gudanar da wani zama na musamman na kungiyar OIC a ranar Litinin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Aljeriya Ahmed Attaf, a wani bangare na tuntubar da yake yi da ministocin harkokin wajen kasashen musulmi kan Gaza.
A yayin tattaunawar tasa, Mista Araghchi ya yi cikakken bayani kan shawarwarin da ya yi a baya-bayan nan da shugabannin kasashen musulmi, da kuma babban sakataren kungiyar OIC, Hussein Ibrahim Taha, da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, don jawo hankalin al’ummar duniya kan “makircin tsarkake kabilanci a Gaza”.
Shugaban diflomasiyyar na Iran ya yi maraba da matakin da Aljeriya ta dauka na nuna goyon baya ga tsayin daka da al’ummar Palastinu suke yi na ‘yantar da kansu daga mamayar Isra’ila.
A makon da ya gabata, Trump ya ce Amurka na neman “karbe” Gaza a wani bangare na shirin da ya gabatar a karkashin sunan “sake gina” yankin Falasdinawa da yaki ya daidaita, inda ya ba da shawarar tilastawa wasu ‘yan Gazan miliyan 2.4 gudun hijira zuwa Masar da Jordan.
Tuni dai Alkahira da Amman suka yi watsi da shirin na Trump na tunzura jama’a.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
Wata kungiya mai suna Grassroots Mobilizers for Better Nigeria Initiative (GMBNI), ta yi Allah wadai da kisan gilla da aka yi wa wani Almajiri a ƙaramar hukumar Gwaram, Jihar Jigawa.
Ƙungiyar ta bayyana matuƙar bakin ciki da ɓacin rai game da wannan cin zarafin da aka yi wa yaron, wanda ya kai ga mutuwarsa cikin mawuyacin hali.
A cewar jami’in yankin Arewa maso Yamma na kungiyar ta GMBNI, Abbas Rufa’i Wangara, rahotanni sun nuna cewa wani Malamin makarantar Allo ya yi wa yaron bulala da har ta kai ga mutuwarsa.
Lamarin ya ƙara muni inda ake zargin Malamin ya yanke kan gawar yaron, ya cire mazakutarsa gabansa na sirri, sannan ya binne gawar a wani ƙaramar rami.
GMBNI ta bayyana wannan aika-aika a matsayin cin zarafin ɗan Adam.
Ƙungiyar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan mamacin, tana mai jaddada cewa babu wani yaro da ya kamata ya fuskanci irin wannan zalunci, musamman a wurin da ake koyar da ilimi da tarbiyya.
GMBNI ta nanata buƙatar gaggawar yin gyara a tsarin ilimin Almajiranci, wanda ya daɗe yana fama da sakaci, cin zarafi, da rashin kulawa.
Ta yi kira ga hukumomi a dukkan matakai da su ɗauki matakan da suka dace don kare Almajirai tare da tabbatar da sun sami ingantaccen ilimi cikin kyakkyawar kulawa.
Ƙungiyar ta kuma bukaci hukumomin tsaro da na shari’a da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da tabbatar da cewa an hukunta wanda ya aikata wannan danyen aiki ba tare da ɓata lokaci ba.
Shugabar GMBNI, Ambasada (Dr.) Fatima Mohammed Goni, ta sake jaddada aniyar ƙungiyar na kare haƙƙin yaran da ke cikin mawuyacin hali.
Ta yi kira ga ƙungiyoyin farar hula, ‘yan kasa da al’ummar duniya baki ɗaya da su haɗa kai wajen neman adalci ga mamacin da kuma tashi tsaye wajen tabbatar da adalci da daidaito ga dukkan yara a Najeriya.
Usman Mohammed Zaria