Iran Ta Yi Allah Wadai Da Barazanar Da Trump Ya Yi Mata
Published: 12th, February 2025 GMT
Iran ta yi kakkausar suka kan barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi na yin amfani da karfi a kan kasar, inda ta bayyana hakan a matsayin barazana da rashin da’a.
A cikin wata wasika da ya aike a wannan Talata zuwa ga shugaban Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhu na dindindin jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya, Amir Saïd Iravani, ya bayyana cewa kalaman na Trump na tada hankali sun sabawa dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.
Trump ya ce zai gwammace ya kulla yarjejeniya da Iran maimakon “harba mata bam fiye da kima,” a wata hira da manema labarai a ranar Asabar.
“Na fi son kulla yarjejeniya da ba za ta cutar da su ba,” in ji shi. “Zan so in yi yarjejeniya da su ba tare da kai musu harin bam ba,” in ji Trump ga jaridar New York Post.
Iravani ya bayyana cewa, kalaman na Trump masu hadari da tayar da hankali sun sabawa dokokin kasa da kasa da kuma Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya, musamman a shafi na 2 (4), wanda ya haramta barazana ko amfani da karfi kan kasashe masu cin gashin kai. »
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
A Gabon, yau Asabar ne Jama’ar kasar suka kada kuri’a domin zaben shugaban kasar, a karon farko bayan kifar da iyalan gidan Bongo daga mulkin kasar.
Janar Brice Oligui Nguema, wanda ya kifar da mulkin Ali Bongo na daga cikin ‘yan takarar dake fafatawa a zaben daga cikin ‘yan takara guda takwas.
Sauran yan takarar sun hada da Firaministan kasar Alain Claude Bilie-by-Nze, wanda ya rike wannan mukami a lokacin mulkin Bongo, da kuma wasu manyan kusoshin tsohuwar jam’iyya mai mulki ta PDG.
Kimanin mutum miliyan daya ne aka tantance su kada kuri’a a zaben, daga cikin jimilar miliyan biyu da rabi na kasar.
A karfe 06:00 na yamma agogon kasar wato 05:00 na yamma agogon GMT, na yau aka tsara rufe rumfunan zaben.
Za a iya fara sanar da sakamakon zaben daga gobe Lahadi.