Aminiya:
2025-02-20@08:54:51 GMT

Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data

Published: 12th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta buƙaci Hukumar Kula da Sadarwa (NCC) ta janye ƙarin kashi 50 na kuɗin waya da data da ta amincewa kamfanonin sadarwa su yi.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ɗan majalisar daga Jihar Bayelsa, Oboku Oforji ya gabatar da ƙudirin kan lamarin.

Majalisar ta ce ƙarin bai kamata ba a wannan lokacin, saboda har yanzu babu tsayayyen layin waya mai sabis mai kyau a cikinsu.

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

A don haka ne majalisar ta buƙaci NCC da Ministan Sadarwa, Bosun Tijani, su dakatar da ƙarin saboda matsin tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fama da shi.

Alƙaluma dai na nuna daga watan Disambar 2023 zuwa yanzu, jimillar ‘yan Najeriya miliyan 224 ne ke amfani da layukan waya.

Alƙaluman sun kuma nuna MTN ne ka kan gaba da kashi 38.79 da adadin kwastamomi miliyan 87, sai Glo da Airtel masu miliyan 61, sai 9mobile mai miliyan 13.9.

Daga cikin kamfanonin kuma, MTN tuni ya fara ɗabbaka ƙarin kashi 50 akan kuɗin data da kiran waya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kamfanonin sadarwa Karin kudin data a Najeriya Majalisar Wakilai Sadarwa

এছাড়াও পড়ুন:

Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof

Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof ya bayyana cewa falasdinawa masu kasa ne zasu fayyace makomar kasarsu, don haka shirin da wasu manya-manyan kasashen duniya suke dashi a kan makomar Falasdinu da Falasdinawa ba dai-dai bane kuma zamu yi yaki da shi.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Teran ta nakalto shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammada Bakir Qolibft yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokoki na kasashen Asia a birnin Baku na kasar Azaibaijan.

Qolibof ya kuma kara da cewa shirin shugaban kasar Amurka yake yi na kwace gaza da kuma inda za’a maida Falasdinawa ba zai kai ga nasara ba.

Qalibof ya yi allawadai wadai da shugaba Trump kan shishigin da yake yi a cikin al-amuran Falasdinawa, da kuma yin watsi da kokarin Falasdinawa a gaza suke yi don kwato kasarsu.

Ya ce Iran ba za ta amince da duk wata kasa mai jin tana da karfi wacce za ta dorawa falasdinawa tunaninsa ba.

Shugaban majalisar ya bayyana cewa yakin da HKI ta fafata da falasdinawa a Gaza, da kuma kungiyar Hizbulla a kasar Lebanon, sun bayyana raunin HKI a fili, wannan duk tare da dukkan tallafin da take samu daga kasashen yamma musamman Amurka.

Daga karshe ya ce dole ne a sami yentacciyar kasar Palasdinu mai zaman kanta nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • An Nuna Nezha 2 A Zama Na Musamman A Hedikwatar MDD Dake Birnin New York
  • Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar Haraji
  • Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi
  • Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
  • Hauhawar farashi ya koma kashi 24 a Nijeriya — NBS
  • Kotu ta hana Gwamnatin Tarayya riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano