Aminiya:
2025-03-23@03:35:15 GMT

Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data

Published: 12th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta buƙaci Hukumar Kula da Sadarwa (NCC) ta janye ƙarin kashi 50 na kuɗin waya da data da ta amincewa kamfanonin sadarwa su yi.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ɗan majalisar daga Jihar Bayelsa, Oboku Oforji ya gabatar da ƙudirin kan lamarin.

Majalisar ta ce ƙarin bai kamata ba a wannan lokacin, saboda har yanzu babu tsayayyen layin waya mai sabis mai kyau a cikinsu.

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

A don haka ne majalisar ta buƙaci NCC da Ministan Sadarwa, Bosun Tijani, su dakatar da ƙarin saboda matsin tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fama da shi.

Alƙaluma dai na nuna daga watan Disambar 2023 zuwa yanzu, jimillar ‘yan Najeriya miliyan 224 ne ke amfani da layukan waya.

Alƙaluman sun kuma nuna MTN ne ka kan gaba da kashi 38.79 da adadin kwastamomi miliyan 87, sai Glo da Airtel masu miliyan 61, sai 9mobile mai miliyan 13.9.

Daga cikin kamfanonin kuma, MTN tuni ya fara ɗabbaka ƙarin kashi 50 akan kuɗin data da kiran waya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kamfanonin sadarwa Karin kudin data a Najeriya Majalisar Wakilai Sadarwa

এছাড়াও পড়ুন:

Turkiya:Fiye Da’Yan Adawa 300,000 Su Ka Yi Zanga-Zanga Nuna Kin Jinin  Tayyib Ordugan

KAmfanin dillancin labarun “al-Somariyya Newas” ya ambato jagoran ‘yan hamayyar siyasa na kasar Turkiya Uzgor Auzal yana fadin cewa: A daren jiya juma’a adadin wadanda su ka fito Zanga-zangar nuna kin jinin shugaba Rajab Tayyib Urdugan sakamakon sauke da kama ‘yan hamayyar siyasa da ya yi kaga kan mukamansu da su ka hada da magajin garin birnin  Istanbul.

Magajin garin Istanbul Imam Uglu ya yi watsi da duk wata tuhuma da aa yi masa ta hannu a cin hanci da rashawa.

Kamfanin dillancin labaran “Reusters” ya nakalto wata majiyar shari’a tana cewa Imam Uglu ya yi watsi da dukkanin thume-tuhumen da aka yi masa masu alaka a cin hanci da rashawa.

Shi dai Imam Uglu zai tsaya takarar shugabancin kasa da Urdugan, kuma ana tsinkayo cewa zai iya lashe zabe.

Jami’ar adawa da Imam Uglu ya fito daga cikinta “ Turkish Republican Party” ta yi Allawadai da kama Imam Uglu, tare da bayyana shi da cewa, bi ta da kulli ne na siyasa kawai.

Bayan kama Imam Uuglu Zanga-zanga ta barke a cikin birane da garuruwa mabanbanta na kasar ta Turkiya  tare da yin tir da abinda ya faru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turkiya:Fiye Da’Yan Adawa 300,000 Su Ka Yi Zanga-Zanga Nuna Kin Jinin  Tayyib Ordugan
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • An gudanar da gagarumar zanga-zangar nuna goyon bayan Falastinu a kasar Jordan
  • Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso
  • Gwamnati Ta Jaddada ƙudirin Kare ‘Yancin Faɗin Albarkacin Baki Da ‘Yancin ‘Yan Jarida
  • Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu