Aminiya:
2025-04-14@17:49:17 GMT

Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data

Published: 12th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta buƙaci Hukumar Kula da Sadarwa (NCC) ta janye ƙarin kashi 50 na kuɗin waya da data da ta amincewa kamfanonin sadarwa su yi.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ɗan majalisar daga Jihar Bayelsa, Oboku Oforji ya gabatar da ƙudirin kan lamarin.

Majalisar ta ce ƙarin bai kamata ba a wannan lokacin, saboda har yanzu babu tsayayyen layin waya mai sabis mai kyau a cikinsu.

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

A don haka ne majalisar ta buƙaci NCC da Ministan Sadarwa, Bosun Tijani, su dakatar da ƙarin saboda matsin tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fama da shi.

Alƙaluma dai na nuna daga watan Disambar 2023 zuwa yanzu, jimillar ‘yan Najeriya miliyan 224 ne ke amfani da layukan waya.

Alƙaluman sun kuma nuna MTN ne ka kan gaba da kashi 38.79 da adadin kwastamomi miliyan 87, sai Glo da Airtel masu miliyan 61, sai 9mobile mai miliyan 13.9.

Daga cikin kamfanonin kuma, MTN tuni ya fara ɗabbaka ƙarin kashi 50 akan kuɗin data da kiran waya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kamfanonin sadarwa Karin kudin data a Najeriya Majalisar Wakilai Sadarwa

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza

Al’ummar Mauritaniya sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da yakin da ake yi a Gaza

A karkashin taken “An rusa Gaza” kuma goyon bayan al’umma ga Falasdinawa abu ne da ya zama wajibi, ba zabi ba, mazauna birnin Nouakchott fadar mulkin kasar Mauritaniya sun gudanar da zanga-zanga domin jaddada bukatar musulmi a ko’ina a duniya su goyi bayan gwagwarmayar da ake yi a Zirin Gaza.

Zanga-zangar dai ta samu halartar kungiyoyin ‘yan jaridu da sauran kungiyoyi da dama, wadanda suka bayyana Allah wadai da shirun da manyan kasashen duniya suka yi, tare da sukar su kan goyon bayan sojojin mamayar Isra’ila.

Wani sheikhin malami dan kasar Mauritaniya ya ce: “Sun sanar da mu irin wannan gagarumin aiki, Allah Ya saka musu da alheri kan irin wannan zanga-zangar da suke yi na goyon bayan wadanda ake zalunta ta hanyar kashe mata da yara da kuma tsofaffi da suke yunkurin kare hakkokinsu.

Masu zanga-zangar sun yi kira da a yanke alaka tsakanin kasarsu da Amurka da duk masu goyon bayan yahudawan sahayoniyya a yakin da suke yi na neman shafe Falasdinawa daga kan doron kasa tare da azabtar da su da masifar yunwa a zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • CMG Ya Kaddamar Da Nuna Fina-Finai Da Shirye-Shiryen Talabijin Na Kasar Sin Masu Inganci A Malaysia
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)