Gwamnatin Jihar Kano Ta Fara Rangadin Tantance Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Published: 12th, February 2025 GMT
Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ta fara rangadin tantancewa a kauyukan jihar, gabanin shirin wayar da kan al’umma game da yaran da ba su zuwa makaranta.
Ziyarar na da nufin gano musabbabin wannan matsala tare da nemo mafita ta hanyar hada kai tsakanin al’umma.
Kididdigar da Asusun yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya fitar na nuna da cewa, Kano tana da kimanin yara 837,479 da ba sa zuwa makaranta, adadi mai ban mamaki da jihar ke kokarin magancewa.
Tawagar tantancewar, karkashin jagorancin jami’a mai kula da ilimin yara mata ta jihar, Hajiya Amina Kassim, ta ziyarci kauyuka da dama, inda ta tattauna da iyaye, da shugabannin gargajiya, da malaman addini.
“Tawagar ta gano muhimman abubuwan da ke haddasa yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankunan karkara, ciki har da talauci, da rashin tsaro, da kuma al’adun zamantakewa”
Mataimakin shugaban kwamitin gudanarwa na makarantun jihar SBMC, Alhaji Garba Adamu Wudil, ya ce ta hanyar hada kai da al’ummomin yankin da masu ruwa da tsaki, gwamnati na da burin kara fahimtar matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta da kuma kokarin samar da ingantaccen ilimi ga kowa da kowa.
Hakimin kauyen Kafin Malamai a karamar hukumar Garko Mukhtar Aliyu da wakilin hakimin kauyen Bange na Wudil Ya’u Ibrahim Bange sun yabawa kokarin gwamnati mai ci na gyara fannin ilimi.
Sun yi kira ga gwamnati da ta kara samar da karin makarantun sakandire a cikin al’umma domin daukar adadin daliban da suka kammala karamar sakandare (JSS) duk shekara.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, rangadin tantancewar wani muhimmin mataki ne na samar da ingantattun dabaru don rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a jihar Kano.
Daga Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: yaran da ba sa zuwa makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora : Kokarin Makiya Na Haifar Da Sabani Ya Ci Tura
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa kokarin da makiya suke yi na haifar da sabani a tsakanin al’ummar kasar ta hanyar yi musu barazana ya ci tura.
Babban tattakin da al’ummar kasar suka yi a ranar 10 ga watan Fabrairu ya nuna cewa barazanar makiya ba ta da wani tasiri a kan wannan kasa da kuma al’ummarta.
Jagoran ya yi ishara da irin gagarumar fitowar al’ummar kasar a cikin jerin gwano da bukukuwan tunawa da cika shekaru 46 da juyin juya halin Musulunci, wanda ya hambarar da azzalumar gwamnatin Pahlavi ta tsohuwar gwamnatin Amurka.
Ayatullah Khamenei ya sake ba da misali da irin dimbin abubuwan da suka faru a lokacin zagayowar nasarar juyin juya halin Musulunci a wannan shekara.
Bayan shekaru arba’in da cin nasarar juyin juya halin Musulunci, a daidai lokacin da ake tunawa da nasarar juyin juya halin Musulunci, dukkanin al’ummar kasar, sojoji, jami’ai, sun fito duk kuwa da irin matsalolin da ake fuskanta.