Gwamnatin Jihar Kano Ta Fara Rangadin Tantance Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Published: 12th, February 2025 GMT
Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ta fara rangadin tantancewa a kauyukan jihar, gabanin shirin wayar da kan al’umma game da yaran da ba su zuwa makaranta.
Ziyarar na da nufin gano musabbabin wannan matsala tare da nemo mafita ta hanyar hada kai tsakanin al’umma.
Kididdigar da Asusun yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya fitar na nuna da cewa, Kano tana da kimanin yara 837,479 da ba sa zuwa makaranta, adadi mai ban mamaki da jihar ke kokarin magancewa.
Tawagar tantancewar, karkashin jagorancin jami’a mai kula da ilimin yara mata ta jihar, Hajiya Amina Kassim, ta ziyarci kauyuka da dama, inda ta tattauna da iyaye, da shugabannin gargajiya, da malaman addini.
“Tawagar ta gano muhimman abubuwan da ke haddasa yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankunan karkara, ciki har da talauci, da rashin tsaro, da kuma al’adun zamantakewa”
Mataimakin shugaban kwamitin gudanarwa na makarantun jihar SBMC, Alhaji Garba Adamu Wudil, ya ce ta hanyar hada kai da al’ummomin yankin da masu ruwa da tsaki, gwamnati na da burin kara fahimtar matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta da kuma kokarin samar da ingantaccen ilimi ga kowa da kowa.
Hakimin kauyen Kafin Malamai a karamar hukumar Garko Mukhtar Aliyu da wakilin hakimin kauyen Bange na Wudil Ya’u Ibrahim Bange sun yabawa kokarin gwamnati mai ci na gyara fannin ilimi.
Sun yi kira ga gwamnati da ta kara samar da karin makarantun sakandire a cikin al’umma domin daukar adadin daliban da suka kammala karamar sakandare (JSS) duk shekara.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, rangadin tantancewar wani muhimmin mataki ne na samar da ingantattun dabaru don rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a jihar Kano.
Daga Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: yaran da ba sa zuwa makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a Ribas
Majalisar Wakilai ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya yi a Jihar Ribas.
Majalisar ta yanke wannan shawara ne a ranar Alhamis, ta hanyar kaɗa ƙuri’a da baki, inda ’yan majalisa 243 suka halarta.
Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a AbujaA matsayin wani ɓangare na matakan dokar ta-ɓaci, majalisar ta bayar da shawarar kafa kwamiti domin dawo da zaman lafiya a jihar.
Hakazalika, majalisar za ta karɓi ragamar gudanar da ayyukan Majalisar Dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida.
Me Ya Sa Aka Ayyana Dokar Ta-ɓaci?Matakin ya biyo bayan rikicin siyasa da ya ƙi ya ƙi cinyewa a Jihar Ribas.
Shugaba Tinubu ya yanke wannan shawara ne sakamakon tashe-tashen hankula da rikicin shugabanci a jihar.
Gwamna Siminalayi Fubara na takun-saƙa da Majalisar Dokokin Jihar da wasu jiga-jigan ’yan siyasa musamman waɗanda ke tsagin tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, lamarin da ya jefa jihar cikin tashin hankali.
Domim shawo kan matsalar, Tinubu ya naɗa Tsohon Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), a matsayin sabon mai kula da jihar.
Hakan ya sa Gwamna Fubara da wasu manyan jami’ai, ciki har da iyalansa, suka bar gidan gwamnatin jihar.
Ana ci gaba da sa ido kan halin da ake ciki a jihar, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da doka da oda a jihar.