Aminiya:
2025-04-14@17:00:04 GMT

Ɗan majalisar Kebbi ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Published: 12th, February 2025 GMT

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Besse/Maiyama daga Jihar Kebbi, Salisu Garba Koko, ya sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Koko, ya sanar da wannan mataki ne cikin wata wasiƙa da ya aike kuma aka karanta a zauren majalisa.

N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – Matashi Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum

Ya bayyana rikicin cikin gida a jam’iyyar PDP a matsayin dalilin da ya tilasta masa barin ta.

Wannan sauya sheƙa ya biyo bayan ficewar wani ɗan majalisar Kaduna, Amos Gwamna Magaji, wanda shi ma ya fice daga PDP sabida rikice-rikice.

Sai dai shugaban marasa rinjaye a majalisar, Kingsley Chinda, ya musanta zargin jam’iyyar na fama da rikice-rikice.

Ya jadadda cewar kowace jam’iyya tana da bambancin ra’ayi, amma hakan ba yana nufin samun rigingimu ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Sauya Sheƙa

এছাড়াও পড়ুন:

Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo

A Gabon, yau Asabar ne Jama’ar kasar suka kada kuri’a  domin zaben shugaban kasar, a karon farko bayan kifar da iyalan gidan Bongo daga mulkin kasar.

Janar Brice Oligui Nguema, wanda ya kifar da mulkin Ali Bongo na daga cikin ‘yan takarar dake fafatawa a zaben daga cikin ‘yan takara guda takwas.

Sauran yan takarar sun hada da Firaministan kasar Alain Claude Bilie-by-Nze, wanda ya rike wannan mukami a lokacin mulkin Bongo, da kuma wasu manyan kusoshin tsohuwar jam’iyya mai mulki ta PDG.

Kimanin mutum miliyan daya ne aka tantance su kada kuri’a a zaben, daga cikin jimilar miliyan biyu da rabi na kasar.

A karfe 06:00 na yamma agogon kasar wato 05:00 na yamma agogon GMT, na yau aka tsara rufe rumfunan zaben.

Za a iya fara sanar da sakamakon zaben daga gobe Lahadi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassa Al-Mujtaba (a) 107
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13