Shugaban kungiyar dalibai ta makarantar (SUG), Comrade Haruna Umar, ya bayyana cewa marigayiya tana cikin shirye-shiryen kammala rajistar ta a makaranta ne ma kafin rasuwarta, kana ya roƙi ɗalibai da su kasance cikin hakuri da lumana, yana mai tabbatar da cewa hukumar makaranta da ta tsaro suna iya ƙoƙarinsu na ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da an yi adalci a kan lamarin.

 

Har ila yau, ya yi kira ga hukumar makarantar da ma Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC), da su girke tudu-tudu na rage gudu a kusa da makarantar domin kaucewa irin hatsarin nan gaba.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa

Wata kungiya mai suna Grassroots Mobilizers for Better Nigeria Initiative (GMBNI), ta yi Allah wadai da kisan gilla da aka yi wa wani  Almajiri a ƙaramar hukumar Gwaram, Jihar Jigawa.

Ƙungiyar ta bayyana matuƙar bakin ciki da ɓacin rai game da wannan cin zarafin da aka yi wa yaron, wanda ya kai ga mutuwarsa cikin mawuyacin hali.

A cewar jami’in yankin Arewa maso Yamma na kungiyar ta GMBNI, Abbas Rufa’i Wangara, rahotanni sun nuna cewa wani Malamin makarantar Allo ya yi wa yaron bulala da har ta kai ga mutuwarsa.

Lamarin ya ƙara muni  inda ake zargin Malamin ya yanke kan gawar  yaron, ya cire mazakutarsa gabansa na sirri, sannan ya binne gawar a wani ƙaramar rami.

GMBNI ta bayyana wannan aika-aika a matsayin cin zarafin ɗan Adam.

Ƙungiyar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan mamacin, tana mai jaddada cewa babu wani yaro da ya kamata ya fuskanci irin wannan zalunci, musamman a wurin da ake koyar da ilimi da tarbiyya.

GMBNI ta nanata buƙatar gaggawar yin gyara a tsarin ilimin Almajiranci, wanda ya daɗe yana fama da sakaci, cin zarafi, da rashin kulawa.

Ta yi kira ga hukumomi a dukkan matakai da su ɗauki matakan da suka dace don kare Almajirai tare da tabbatar da sun sami ingantaccen ilimi cikin kyakkyawar kulawa.

Ƙungiyar ta kuma bukaci hukumomin tsaro da na shari’a da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da tabbatar da cewa an hukunta wanda ya aikata wannan danyen aiki ba tare da ɓata lokaci ba.

Shugabar GMBNI, Ambasada (Dr.) Fatima Mohammed Goni, ta sake jaddada aniyar ƙungiyar na kare haƙƙin yaran da ke cikin mawuyacin hali.

Ta yi kira ga ƙungiyoyin farar hula, ‘yan kasa da al’ummar duniya baki ɗaya da su haɗa kai wajen neman adalci ga mamacin da kuma tashi tsaye wajen tabbatar da  adalci da daidaito ga dukkan yara a Najeriya.

Usman Mohammed Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • Mutane Da Dama Ne Ake Jin Tsoron Sun Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Daukar Gas Ta Yi Bindiga A Kan Gadar Karu A Birnin Abuja