An yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga a Kaduna
Published: 12th, February 2025 GMT
Mazauna Ungwan Ate da ke Ƙaramar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna, sun fito kan tituna domin yin zanga-zanga kan yawaitar hare-haren ’yan bindiga da satar jama’a da suka addabi yankinsu.
Masu zanga-zangar sun toshe hanyar Ungwan Ate zuwa Ungwan Mission da ke kan babbar hanyar Kaduna zuwa Kachia.
Ɗan majalisar Kebbi ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – MatashiSun kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don kare rayukansu da dukiyoyinsu.
Wani daga cikin masu zanga-zangar da ya zanta da Aminiya, ya ce ’yan bindiga sun shiga Ungwan Ate a daren ranar Talata, inda suka shafe sama da sa’o’i biyu suna cin karensu ba babbaka, tare da sace mutum ɗaya daga ƙauyen.
“Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.
“’Yan bindiga suna yawan kawo mana hari a duk lokacin da suka ga dama. Gwamnati da hukumomin tsaro su gaggauta ɗaukar mataki kafin mu ƙare,” in ji shi.
Wani mazaunin yankin ya ce matsalar tsaro a Kachia ta kai ga mutane ba sa iya zuwa gonakinsu ko barci cikin kwanciyar hankali.
“Gwamnati ta ce ta yi sulhu da ‘yan bindiga, amma kullum ana kashe mu a Kachia.
“Mutane da dama na cikin daji suna shan wahala kan laifukan da ba su san komai a kansu ba,” in ji shi cikin fushi.
Masu zanga-zangar sun ce ’yan bindiga sun mayar da yankin filin daga, lamarin da ya sa suka tsinci kansu cikin tsananin fargaba da damuwa.
“Ba ma iya zuwa gona, alhali yawancinmu da noma muka dogara,” in ji wani daga cikin masu zanga-zangar.
“Ba ma iya yin barci cikin kwanciyar hankali. Ana so a ƙarar da mu ne?”
Zanga-zangar ta biyo bayan hare-hare da yawaitar sace-sacen mutane a Ƙaramar Hukumar Kachia.
Ƙauyuka irin su Gadanji, Ungwan Wage, Ungwan Alhaji, Agunu Dutse, Maro da Ungwan Dauje na fama da hare-haren ’yan bindiga ba dare ba rana.
Mazauna yankin sun ce duk da kiraye-kirayen da suke yi ga mahukunta, babu wani matakin tsaro da aka ɗauka domin kare su daga hare-haren.
A halin da ake ciki, mazauna yankin na ci gaba da roƙon gwamnati da hukumomin tsaro da su kawo musu ɗauki domin dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai amsa kiran waya ba.
Ga hotunan yadda zanga-zangar ta gudana:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hare hare Tsaro zanga zangar yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
Shugaban kungiyar Hamas Khalilul-Hayyah, ya fadi cewa; A ranakun Alhamis da Asabar masu zuwa ne za a mikawa ‘yan mamaya fursunoni rayayyu da kuma wasu gawawwaki a cikin bude wani shafin na musaya.
A jiya Talata ne dai Khalilul-Hayyah ya sanar da cewa, a bisa yadda aka cimma matsaya a musayar farko da aka yi, a cikin mako na shida daga kulla yarjejeniya, za a shiga wani sabon shafin na gaba na musayar fursunoni.
Khalil Hayya ya kuma ce a ranar Asabar din mai zuwa ne za a mika sauran fursunoni rayayyu da su ka saura, kamar yadda aka cimma matsaya da adadinsu shi ne 6, biyu daga cikinsu ana rike da su ne tun 2014, yayin da ‘yan mamaya za su saki sauran fursunonin da suke rike da su.
Shugaban na kungiyar Hamas ya bayyana hakan da cewa, yana nuni da yadda kungiyar take aiki da yarjejeniya, tare da yin kira da a tilasta HKI ta yi aiki da sharuddan yarjejeniyar ba tare da jan kafa ba. Haka nan kuma ya bayyana cewa kungiyar ta Hamas tana cikin shirin ko-ta –kwana na shiga shafi na gaba wanda shi ne dakatar da yaki da kuma janyewar sojojin mamayar daga Gaza.