Kasar Sin Ta Yi Kiran Samar Da Ci Gaba Da Tsaro Bai-daya A Fannin Fasahar AI.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Lijiang Na Lardin Yunnan

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadi a birnin Lijiang na lardin Yunnan dake kudu maso yammacin kasar Sin da yammacin jiya, inda ya ziyarci lumbunan samar da furanni masu aiki da sabbin fasahohi na zamani da tsohon garin Lijiang, don fahimtar yadda ake raya aikin gona na musamman mai la’akari da yanayin wurin, da yadda ake gaggauta karewa da amfani da kayayyakin al’adu na tarihi da aiwatar da ra’ayin dunkulewar al’umomin Sinawa.

Lambun renon furanni mai aiki da fasahar zamani na Lijiang na da fadin hekta 73.3, wanda ya hada aikin shuka da sufurin furanni da yawon bude ido tare, kuma ya habaka aikinsa zuwa harhada man furanni da samar da busassun furanni da sarrafa abinci mai hade da furanni da sauransu. A kan yi jigilar kayayyakin da ya kan samar ba kadai zuwa manyan birane kamar Beijing da Shanghai da Guangzhou da sauransu ba, har da kai su kasashen waje kamar Japan da Vietnam da Rasha da sauransu, matakin da ya samar da karin guraben aikin yi kimanin 300 a kauyukan dake kewayensa.

Yayin ziyararsa, Xi Jinping ya ce, “ku gudanar da wannan aiki da kyau, wanda ya dace da alkiblar da ake bi na zamanatar da aikin gona. Ina fatan rayuwarku za ta yi kyau tamkar kyawawan furanni.”

Garin gargajiya na Lijiang na da tarihi fiye da shekaru 800. Shugaba Xi ya ce, al’adu da shimfidar wurin da hikimomin al’ummar wannan wuri na jawo hankalin mutane sosai, kuma haduwar al’adu da sha’anin yawon bude ido na ciyar da tattalin arzikin wuri gaba. Ya kara da cewa, ya kamata a raya wannan sha’ani bisa hanya mai kyau da dorewa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Za Ta Kara Daidaita Matakan Jawo Jarin Waje
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki
  • An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno
  • Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama
  • Xi Ya Bukaci A Bude Sabbin Hanyoyin Samun Ci Gaba Yayin Rangadinsa A Lardin Yunnan
  • Kungiyar M-23 Ta Kasar Kongo Ta Kara Nusawa Gaba A Don Mamaye Karin Yankuna A Gabacin Kongo
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Lijiang Na Lardin Yunnan
  • Sabon Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano Yayi Alkawarin Inganta Tsaro