Al’ummar Jigawa Sun Bukaci Gwamnati Ta Yi Koyi Da Shirin NG-CARES Wajen Tallafawa Mabukata
Published: 12th, February 2025 GMT
Al’ummar Jihar Jigawa sun yi kira ga Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi da ya yi amfani da kyawawan tsarin da gaskiya wajen zabar wadanda za su ci gajiyar shirye-shiryen bada tallafin karfafa sana’o’i.
Sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi amfani da tsarin bayar da tallafin karfafa al’umma ma gwamnatin tarayya na (FADAMA) a dukkan shirye shiryenta ta bada tallafi, domin ganin al’ummar jihar sun ci gajiyar ayyukan gwamnati.
Wani shugaban al’ummar yankin Walewale a karamar hukumar Garki, Malam Haruna Abdullahi, ya ce, hanyar da shirin FADAMA na gwamnatin tarayya ya yi amfani da ita ya tabbatar da cewa tallafin ya isa ga masu bukata.
A cewarsa, tsarin ya kawar da son zuciya da siyasa, wanda hakan ya yi tasiri matuka ga al’umma.
“Mun ga yadda shirin FADAMA kkarkashin shirin gwamnatin tarayya na G-CARES ya samu damar tallafawa manoma na hakika da sauran mutanen da suka cancanta, idan aka yi amfani da wannan tsari a duk wasu tsare-tsare na karfafawa, zai kawo ci gaba na hakika a jihar Jigawa.”
Wani mazaunin garin, Usman Alhaji na Arbun a karamar hukumar Auyo, ya kara da cewa daukar tsarin zaben wadanda suka cancanta zai kara wa gwamnatin jihar kima a idon jama’a.
Sun bukaci Gwamna Namadi da ya yi amfani da wannan tsari ga sauran shirye-shiryen karfafawa a jihar, tare da tabbatar da cewa tallafin gwamnati na isa ga wadanda suka fi bukata.
Shi ma da yake jawabi, shugaban kwamitin riko na shirin FADAMA CARES, Dakta Saifullahi Umar ya bayyana cewa, shirin na NG-CARES an tsara shi ne domin dakile matsin tattalin arzikin da annobar Corona
. ta haifar.
Dakta Saifullahi ya ce, abu na 2 wanda aka aiwatar ta hanyar shirin FADAMA, yana mai da hankali ne kan tallafin noma da inganta rayuwa, ta hanyar yin amfani da kyakkyawan tsari wajen zabo wadanda suka dace su ci gajiyar shirin.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
Al’ummar garin Idi Araba da ke Ƙaramar Hukumar Munshin a Legas sun wayi gari da fashewar wani abu mai ƙarar gaske, wanda ya tayar da gobara a wani garejin ’yan gwangwan da ke unguwar.
Lamarin da ya faru ranar Alhamis na makon jiya ya yi sanadiyar mutuwar wani da ke sana’ar gwangwan mai suna Najib Zakiru, da ƙonewar sashin wani gida da ke daura da wajen da ’yan gwangwan ke sana’arsu.
Aminiya ta ziyarci inda lamarin ya faru unguwar IdiAraba, ta kuma zanta da mammalakin wajen sana’ar ta ’yan gwangwan, Alhaji Haruna Musa, wanda kuma shi ne shugaban masu sana’ar a yankin, inda ya shaida wa Aminiya cewa, suna zaune sai suka ji wata irin ƙara mai karfi, ko da suka zo wajen sai suka tarar da wuta ta tashi.
“Da muka zo mun yi ƙoƙarin kashe wutar, da jami’an ’yan sanda suka zo, sun fito da wasu bamabamai na soji guda biyu suka ce daya daga cikin bama-baman ne ya fashe. Wannan ne ya sa suka gayyato ƙwararrun jami’an tsaro a sashen kwance bam, suka zo, suka yi bincike, suka tafi da bama-baman.
“Wannan da Allah Ya yi wa cikawa shi ne ya taho da bama-baman kuma yana kokarin fasa guda daga cikinsu ne abun ya tashi, ya halaka shi, wanda zuwan jami’an tsaro ne suka sa aka killace wajen, aka rufe, aka hana mutane shiga, kuma haka ne ya janyo wutar da ba ta mutu ba, ta shafi wani gida da ke gefen wajen, inda ta kone ɗakuna biyar lamarin da ya janyo mutane gidan suka yi asarar kayayyakinsu da kuma mutsuguninsu”, in ji shi.
Haruna Musa ya shaida cewa, mutumin da hadarin ya rutsa da shi magidanci ne kuma ya bar mace guda da ’ya’ya biyu. Haka kuma baya ga shi babu wani da ya jikkata a sakamakon hadarin, ba kamar yadda ake faɗa a wasu jaridu ba cewa, mutum uku sun jikkata. Ya ce tuni aka yi jana’izarsa a bisa jagorancin Sarkin Hausawan IdiAraba, Alhaji Hassan Auyo.
“yanzu haka mutanen da wutar ta lalata wa gida ba su da wajen kwana, kuma yawancinsu mata ne zawarawa da tsofaffi da yaransu kanana. Mun yi magana da masu sana’ar gwagwan din domin a gyara masu wajen zamansu. Muna fatan mahukunta sun dubi wannan abu a matsayin hadari ne da ya auku, su kuma ba mu dama mu ci gaba da sana’armu. Muna jan kunnen manbobinmu, su guji kayayyaki masu hadari”, In ji shi.
Aminiya ta zanta da matan da suka rasa muhallinsu sakamakon gobarar da ta biyo bayan fashewar bam din. Maman Shahid da wutar ta kone kayan dakinta kurmus, ta shaida wa Aminiya cewa, ‘‘da fari ina kwance a kan gado ne sai karar bam din ta riguzo da rufin silin dakina suka zubo kuma sai na taso na fito daga dakin. Bayan nan kuma
ina zaune a waje ina kokarin yi wa yara abinci sai yaro ya ce, Umma hayaki. Ba mu yi aune ba sai ga wuta ta tashi, ta kone mana dakuna. A lokacin da na yi yunkurin fitar da tukunyar gas din da nake girki, bayan wannan duk kayanmu sun kone, yanzu haka rabe-rabe muke yi wajen da za mu kwanta tare da ‘ya’yanmu”, In ji ta.
Hakazalika, Malama Talatu da ita ma lamarin ya rutsa da ita ta shaida wa Aminiya cewa, tana wajen kasuwancinta na abincin da take dafawa, ta sayar lokacin da labarin ya riske ta, ta ce kayan ta da ke dakin duk sun kone ba su tsira da komai ba sai kayan da ke jikinsu, inda ta mika kokan bara ga mahukunta da masu hannu da shuni domin su taimaka masu.
A nata bangaren Malama Sa’adatu da aka fi sani da Maman
Fati cewa ta yi babu abun da za su ce sai dai su yi wa Allah Madaukakin Sarki godiya kasancewar babu wanda ya jikkata a cikin gidan nasu duk da cewa akwai tarin yara kanana da mata. “Wannan abin godiya ne, dukiya kuma da sauran kayan da muka rasa tunda dai muna da sauran kwana a gaba ai idan da rai akwai rabo. Babbar damuwarmu a yanzu ita ce wajen kwana, inda muke rabawa, mu kwana daban, inda yaranmu ke kwana daban. Muna fatan a gyara mana wajen kwana, mu samu inda za mu kwanta mu da yaranmu”, in ji ta.
Mista Olarewaju shi ne mamallakin gidan da gobarar ta kone, ya shaida wa Aminiya cewa, abun da ya fi damun sa shi ne halin da ’yan hayar da ke cikin gidansa. “Yanayin wahalhalun da ’yan hayarmu suka shiga shi ya fi damuna, domin mu gida ne ya kone za kuma a iya gyara mana, amma su sun yi asarar kayayyakinsu, kuma yanzu haka ba su da wajen kwana su da yaransu. Haka kuma lokaci ne na damuna, ka ga abun a tausaya masu ne, don haka muna kira ga mahukunta da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa (NEMA) da su zo, su dubi halin da mutanen ke ciki, talakawa ne marasa karfi, yawancinsu ma zawarawa ne da tsofaffi, don haka suna neman agaji. Mu mun dauki wannan abu a matsayin hatsari ko ibti’la’i kuma muna zaune lafiya da Hausawa babu wata matsala a tsakankaninmu da su,” in ji shi.
A zantawar Aminiya da Sarkin
Hausawan Idi-Araba, Alhaji Hassan Abubakar Auyo ya shaida wa Aminiya cewa, sun sami labarin cewa dan gwangwan din da lamarin ya rutsa da shi ya tsinto bamabaman ne guda uku a wata kwata mai zurfi da ke bayan barikin soji na Ikeja, inda shekara 20 da suka wuce aka sami hadarin tashin bamabamai a Legas.
“Wannan wajen da sojin suka yi sharar bama-baman an samu wadanda suka watse jikin wannan kwata mai zurfi, mun sami labarin a nan ne ya tsinto bama-baman, ka san su ‘yan gwangwan da kayan karfe, ya zo, ya yi ta kokarin ya yanka abun ya ci tura, domin ba zallar karfe ba ne, daga nan ya sami guduma ya yi ta dukan bam din da ita, har ya kai ga ya ta shi, ya kuma yi masa mummunan lahani, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwarsa, kuma bayan da labari ya zo mana, mun yi masa sutura bayan ‘yan sanda da ke bincike suka aminta da hakan. A kan wannan lamari babu irin jami’an tsaro da lamarin ya shafa da ba su zo nan ba, mun tattauna kuma mun shiga bincike ka’in da na’in, mun kuma gano lamarin ba shi da alaka da ta’addaci ko wani abu makamancin haka, kuma za mu dauki mataki domin kare afkuwar irin wannan a nan gaba. Don haka za mu yi zama na musamman mu yi taro da jami’an tsaro da shugabaninn ’yan gwangwan domin kawo tsaretsaren da za su tsaftace sana’ar domin zaman lafiyarsu da ta jama’a baki daya,” in ji shi.