Al’ummar Jigawa Sun Bukaci Gwamnati Ta Yi Koyi Da Shirin NG-CARES Wajen Tallafawa Mabukata
Published: 12th, February 2025 GMT
Al’ummar Jihar Jigawa sun yi kira ga Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi da ya yi amfani da kyawawan tsarin da gaskiya wajen zabar wadanda za su ci gajiyar shirye-shiryen bada tallafin karfafa sana’o’i.
Sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi amfani da tsarin bayar da tallafin karfafa al’umma ma gwamnatin tarayya na (FADAMA) a dukkan shirye shiryenta ta bada tallafi, domin ganin al’ummar jihar sun ci gajiyar ayyukan gwamnati.
Wani shugaban al’ummar yankin Walewale a karamar hukumar Garki, Malam Haruna Abdullahi, ya ce, hanyar da shirin FADAMA na gwamnatin tarayya ya yi amfani da ita ya tabbatar da cewa tallafin ya isa ga masu bukata.
A cewarsa, tsarin ya kawar da son zuciya da siyasa, wanda hakan ya yi tasiri matuka ga al’umma.
“Mun ga yadda shirin FADAMA kkarkashin shirin gwamnatin tarayya na G-CARES ya samu damar tallafawa manoma na hakika da sauran mutanen da suka cancanta, idan aka yi amfani da wannan tsari a duk wasu tsare-tsare na karfafawa, zai kawo ci gaba na hakika a jihar Jigawa.”
Wani mazaunin garin, Usman Alhaji na Arbun a karamar hukumar Auyo, ya kara da cewa daukar tsarin zaben wadanda suka cancanta zai kara wa gwamnatin jihar kima a idon jama’a.
Sun bukaci Gwamna Namadi da ya yi amfani da wannan tsari ga sauran shirye-shiryen karfafawa a jihar, tare da tabbatar da cewa tallafin gwamnati na isa ga wadanda suka fi bukata.
Shi ma da yake jawabi, shugaban kwamitin riko na shirin FADAMA CARES, Dakta Saifullahi Umar ya bayyana cewa, shirin na NG-CARES an tsara shi ne domin dakile matsin tattalin arzikin da annobar Corona
. ta haifar.
Dakta Saifullahi ya ce, abu na 2 wanda aka aiwatar ta hanyar shirin FADAMA, yana mai da hankali ne kan tallafin noma da inganta rayuwa, ta hanyar yin amfani da kyakkyawan tsari wajen zabo wadanda suka dace su ci gajiyar shirin.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
Gwamnatin Jihar Jigawa ta dauki matasa fiye da 6,000 aiki a fannoni daban-daban a fadin jihar, a kokarinta na ganin ta inganta rayuwarsu.
A saboda haka ne ma matasan da aka dauka aikin suka karrama Gwamnan Jihar, Malam Umar Namadi, bisa kokarinsa na samar da ayyukan yi da bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.
Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ruwaito cewa, taron karramawar, wanda aka gudanar a gidan Gwamnati dake Dutse Babban Birnin Jihar, ya hada da wadanda suka ci gajiyar shirye-shiryen gwamnati da suka hada da J-Teach, da J-Agro, da J-Health, da J-Millionaires, da sabbin likitocin da aka dauka aiki a bangaren lafiya.
A yayin taron, kowanne rukuni ya mika lambar yabo ga Gwamna Umar Namadi don nuna godiya bisa kokarinsa na ci gaban matasa tare da sharbar romon dimokradiyya.
A jawabin sa, Gwamna Umar Namadi ya nuna matukar farin cikinsa da wannan karramawar da matasan suka yi masa.
Yana mai cewar wannan girmamawar ba tasa ce kadai ba, ta daukacin al’ummar Jihar Jigawa ce gaba daya ba shi kadai ba.
A don haka, ya yaba wa matasan bisa jajircewarsu wajen kafa kyakkyawar rayuwa nan gaba, da kuma taimakawa ci gaban al’umma.
Malam Umar Namadi, ya yi nuni da cewar, matasan Jigawa sun nuna kwarewa da kishin kasa wajen tabbatar da ci gaban jihar.
Yana mai cewar, shakka babu, da irin wannan himma da kwazon matasa, jihar za ta ci gaba da samun ci gaba a fannoni da dama.
Sai dai kuma, Namadi ya bukaci matasan da su ci gaba da kokari wajen bunkasa jihar, yana mai jaddada cewar ci gaban Jigawa na hannun al’ummarta.
Ya kuma tabbatar da kudirin gwamnatinsa na kara samar da damarmaki ga matasa, ta hanyar daukar aiki, da kuma bunkasa tattalin arziki, domin tabbatar da kyakkyawar makoma ga jihar.
Taron ya samu halartar Kakakin Majalisar dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin da Sakataren Gwamnatin, Malam Bala Ibrahim da kwamishinoni da sauran jami’an gwamnatin Jihar.
Usman Mohammed Zaria