Hukumar kula da ‘yan sama jannati na kasar Sin (CMSA), a yau Laraba, ta bayyana sunayen tufafin ‘yan sama jannati da motar zirga-zirga a duniyar wata na aikin binciken wata na kasar.

CMSA ta ce, an sa ma tufafin na ‘yan sama jannati suna Wangyu, wanda ke nufin kallon duniyar sama, kuma ya yi daidai da sunan tufafin da ‘yan sama jannati su kan sa lokacin da suka fita daga tashar sararin samaniya, wato Feitian, wanda ke nufin tashi zuwa sararin samaniya.

Wata Ɗalibar Kwalejin Fasaha Ta Tarayya Da Ke Bauchi Ta Rasa Ranta A Haɗarin Mota Yawan Motocin Da Sin Ta Fitar Zuwa Ketare A 2024 Ya Karu Da Kaso 23%

Kazalika, sunan motar zirga-zirga a duniyar wata shi ne Tansuo, wanda ke nufin binciken gaibu. Hukumar ta ce, wannan sunan yana nuna aikin da motar ke yi, da darajarta wajen taimaka wa jama’ar kasar Sin wajen gano ababen al’ajabi na duniyar wata.

A halin yanzu, ayyukan bincike da suka shafi Wangyu da Tansuo suna ci gaba yadda ya kamata, a cewar CMSA. (Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan sama jannati a duniyar wata

এছাড়াও পড়ুন:

 Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a

Sojojin HKI sun kai wasu hare-hare akan sansanin sojan Sanamain dake gundumar Dara’a a kudancin kasar Syria.

Tashar talabijin din da “ Akhbariyyah” ta Syria ta sanar a yau Litinin cewa; sojojin Isra’ila sun kai hari akan sansanin soja na “Sanamain” wanda yake a gundumar Dar’a, kuma an ga jiragen sama na ‘yan mamaya masu yawa suna shawagi a samaniyar yankin.

Wata majiyar ta Syria ta kuma ambaci cewa; sojojin na HKI sun kursa cikin garin Mu’arrah, tare da  yin kutse cikin gidaje masu yawa a ciki da gudanar da bincike a cikinsu.

A yankin Kunaidhara ma an ga sojojin na mamaya suna yin kutse, haka nan kuma sun kai hari akan filin saukar jiragen sama na Tpor, da kuma wani filin saukar jiragen sama na soja a Tadammur.

Tun bayan da gwamnatin Basshar Assad ta fadi ne dai HKI ta bude kai wa makamai da cibiyoyin sojan kasar hare-hare babu kakkautawa. A cikin kwanakin farko na faduwar gwamnatin Asad, sojojin HKI sun sanar da cewa sun rusa tsakanin kaso 70% zuwa 80% na jumillar makaman da Syria take da su, na sama, kasa da na ruwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Siyo Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Ukraine: Tawagogin Rasha da Amurka sun kammala tattaunawa a Saudiyya
  • An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja
  •  Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
  • Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba
  • Amurka ta sake kai hare-hare Yemen
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila