Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya kara jaddadawa Sarkin Jordan Abdullahi II kan shirinsa na kwace yankin Gaza daga hannun Falasdinawa, sannan ya maida shi wurin shakatawa, da kuma kan cewa kasar Jordan da Masar ne zasu dauki nauyin kula da Falasdinawa kimani miliyon 2 a Gaza a cikin kasashen su.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Trump yana fadar haka a ganawarsa da Sarkin a birnin Washington a yau Laraba.

A nashi bangaren Sarkin kasar ta Jordan ya bayyana cewa yana ganin kasashen larabawa zasu dauki mataki guda ne a cikin wannan al-amarin, sannan zasu ji ta bakin Yerima Muhammad  bin Salman na kasar Saudiya da kuma Shugaba Abdul Fattah Assisi na kasar Masar, wadanda suke da shawarorin da zasu gabatar dangane da wannan matsalar.

Sarkin ya kara da cewa a halin yanzu dai kasarsa za ta dauki yara kanana kimani 2000 marasa lafiya, wadanda suke fama da cutar kansa a Gaza don jinyarsu a kasar Jordan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv

Dakarun Falasdinawa sun mayar da martani ga kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa fararen hula bayan sake dawo da yakin Isra’ila a kan al’ummar Gaza, inda suka harba rokoki zuwa Tel Aviv.

Al-Qassam Brigades, reshen soji na kungiyar gwagwarmayar Islama ta Hamas, ta sanar a wannan  Alhamis cewa, ta yi ruwan makamai masu linzami samfurin M90 a kan birnin Tel Aviv, a matsayin mayar da martani ga kisan kiyashi da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi kan fararen hula a zirin Gaza.

Sojojin mamaya na Isra’ila sun tabbatar da cewa sun gano wasu rokoki guda uku da aka harba daga Gaza zuwa tsakiyar Falasdinu da suka mamaye, tare da jin karar makamai a sararin samniyar Tel Aviv, Gush Dan, da matsugunan yahudawa da ke kewaye.

Isra’ila bat a mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, kamar yadda ta yi fatali da mataki na biyu na yarjejeniyar , tare da sanya wasu sharudda da gangan domin matsin lamba a kan kungiyoyin  gwagwarmayar Falasdinu.

Isra’ila Ta sake sabunta kai hare-hare a zirin Gaza, inda ta kai hari a wurare daban-daban na yankin tun daga kwanaki biyu zuwa uku da suka gabata har zuwa yau.

Hare-haren na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun yi sanadin shahadar daruruwan fararen hula, galibi mata da kanan yara, tare da jikkata wasu da dama .

Wakilin Al-Mayadeen ya tabbatar da cewa sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake raba arewacin Gaza daga tsakiya da kuma kudancin yankin, inda suka sake kwace iko da yankin Netzarim.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gudanar da gagarumar zanga-zangar nuna goyon bayan Falastinu a kasar Jordan
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • A cikin kwanaki 3 Falasdinawa 605 sun yi shahada a kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Miyetti Allah A Filato
  • Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza
  • Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Falasdinawa Ba Za Su Bar Kasarsu Ba, Ko Da Son Ransu Ko Da Karfi