Kungiyar yan ta’adda ta Daesh ta dauki alhakin harin da aka kai a lardin Kunduz na arewacin kasar Afganistan, wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane akalla 5 da kuma raunata wasu da dama.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto “Daesh Khorasan” tana fadar haka a shafinta na sadarwa, bayanda wani dan ta’adda ya tarwatsa kansa a kusa da wani banki a garin Kunduz, wanda ya halaka shi ya kuma yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla guda biyar.

Labarin ya kara da cewa an kai harin kunan bakin wakenne da misalign karfi 8:35 na safe a yau Laraba, wato 4:05 na safe agogin GMT.

Mai gidan bankin da kuma wasu mutane 4 daga cikin akwai fararen hula da kuma wani mamba a jam’iyya mai mulkin kasar, ta kungiyar Taliban.

Kakakin yansandan lardin Kunduz Jumma Uddin Khakasr ya ce: Banda wadanda suka rasa rayukansu, akwai mutane 7 da suka ji rauni. Amaq ya ce, sun tada bom din ne kusa da jami’an yansanda na lardin wadanda suke jiran karban albashinsu.

Kungiyar ta ce, daruruwan mutane ne suka kashe a harin. Kungiyar Daesh Khurasan dai ta sha daukar alhakin kai hare-hare iri wannan a kasar ta Afganistan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza

Jami’an lafiya a Gaza, sun ce akalla mutane 1,563 ne aka kashe tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki a Zirin tun daga ranar 18 ga watan Maris, yayin da al’amuran jin kai ke kara ta’azzara a Gaza.

Adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa Gaza tun bayan da Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas ta Falasdinu a watan jiya ya zarce 1,560 a cewar jami’an kiwon lafiya.

A cikin wata sabuwar sanarwa da ta fitar yau Asabar, ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce hare-haren Isra’ila sun kashe akalla mutane 21 a cikin sa’o’i 24 na baya-bayan nan.

An kashe mutane 50,933 tare da raunata 116,045 tun farkon yakin a watan Oktoban 2023, in ji ma’aikatar a alkalumman data sabunta.

A cewar hukumar ‘yan gudun hijira ta Falasdinawa UNRWA, kimanin Falasdinawa 400,000 ne aka tilastawa barin muhallansu a fadin Gaza tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta fara aiki a watan Janairu ta ruguje kusan wata guda da ya gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  •  Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?