Kungiyar yan ta’adda ta Daesh ta dauki alhakin harin da aka kai a lardin Kunduz na arewacin kasar Afganistan, wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane akalla 5 da kuma raunata wasu da dama.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto “Daesh Khorasan” tana fadar haka a shafinta na sadarwa, bayanda wani dan ta’adda ya tarwatsa kansa a kusa da wani banki a garin Kunduz, wanda ya halaka shi ya kuma yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla guda biyar.

Labarin ya kara da cewa an kai harin kunan bakin wakenne da misalign karfi 8:35 na safe a yau Laraba, wato 4:05 na safe agogin GMT.

Mai gidan bankin da kuma wasu mutane 4 daga cikin akwai fararen hula da kuma wani mamba a jam’iyya mai mulkin kasar, ta kungiyar Taliban.

Kakakin yansandan lardin Kunduz Jumma Uddin Khakasr ya ce: Banda wadanda suka rasa rayukansu, akwai mutane 7 da suka ji rauni. Amaq ya ce, sun tada bom din ne kusa da jami’an yansanda na lardin wadanda suke jiran karban albashinsu.

Kungiyar ta ce, daruruwan mutane ne suka kashe a harin. Kungiyar Daesh Khurasan dai ta sha daukar alhakin kai hare-hare iri wannan a kasar ta Afganistan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU Reshen Jami’ar KASU Ta Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani

“Kungiyar malaman jami’o’i, reshen KASU na son sanar da jama’a cewa, majalisar zartaswarta ta kasa ta amince da bukatar reshen kungiyar na tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar, 18 ga Fabrairu, 2025.

 

“Majalissar ta yi watsi da alkawuran da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka na rashin tabbaci, da cikakkun bayanai, da kuma lokacin da za a iya aiwatar da alkawuran kan biyan hakkokin mambobin kungiyar,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • ASUU Reshen Jami’ar KASU Ta Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno
  • Da Dama Sun Rasu Yayin Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga Hari A Katsina
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
  • Masu Alaka