A lokacinda yake ganawa da masana masu fasaha a masana’antun makamai na kasar da kuma manya-manyan Jami’an sojojin Kasar Iran, Jagoran Juyin Juya Halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana cewa fitowar mutane a zanga-zangar cika shekaru 46 da nasarar juyin juya halin musulunci a kasar, a ranar litinin da ta gabata, wata alama ce ta hadin kan mutanen kasar Iran, har’ila yau jawabi ne ga barazanar da makiya JMI suke mata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana fadar haka bayan ya zagaya ya ga sabbin makamai wadanda masana’antun makamai na kasar suka kera. Ya kuma yaba da irin ci gaban da masana’antun suka samu.

Imam Khaminae ya kuma yaba da ayyukan da masu fasaha da suka kerasu wadannan makamai.

Sabbin makaman da aka baje kolinsu dai, sun hada da garkuwan makamai masu linzami wadanda zasu iya kare sararin samaniyar kasar.

Da kuma ci gaban da aka samu a bangaren garkuwan sararin samaniyar kasar. Har’ila yau da kuma ci gaban da aka samu a bangaren sojojin ruwa.

Daga karshe jagoran ya jinjinawa ma’aikatar tsaron kasar kan irin ci gaban da aka samu, musamman a dai dai lokacinda kasar take fuskantar Barazana. Daga karshe yace: Lalle su zage dantse don gani barazan da kasar take fuskanta a yanzu, da kuma nan gaba sun magancesu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Bikin “Tafiya A Kasar Sin Bisa Ga Fina-finan Kasar”

Bisa ga yadda wasu fina-finan kasar Sin ke samun karbuwa a kasuwannin kasa da kasa, ciki har da fim din “Ne Zha 2”, a yau Litinin an kaddamar da bikin “Tafiya a kasar Sin bisa fina-finan kasar” a gidan tarihi na fina-finai na kasar Sin dake nan birnin Beijing, wanda hukumar kula da fina-finai ta kasar Sin da babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) suka shirya, kuma gidan talabijin na kasa da kasa na kasar Sin (CGTN) da cibiyar shirye-shirye ta tashar fina-finai suka karbi bakuncinsa.

Bikin wanda ya fi mayar da hankali kan gudanar da ayyukan tallata fina-finai da yawon shakatawa ta hanyar nuna fina-finan kasar Sin a ketare, da shirya bikin nune-nunen fina-finan kasar Sin a ketare, da kuma bikin nune-nunen fina-finai na cikin gida da na ketare, yana neman fadakar da masu kallon fina-finai na ketare a kan yanayin kasar Sin, tare kuma da jawo masu yawon shakatawa na ketare su zo kasar Sin don kara fahimtar kasar. (Mai fassara Bilkisu)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • IRGC Ta Kaddamar Da Sabbin Makamai A Atisayen Da Take Yi A Halin Yanzu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alhinin Rasuwar Edwin Clark
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Barazanar Makiya Kan Iran Ba Zata Yi Nasara Ba
  • Kasar Iran Zata Aika Da Tawaga Mai Karfi Zuwa Jana’izar Sayyid Nasarallah
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • An Kaddamar Da Bikin “Tafiya A Kasar Sin Bisa Ga Fina-finan Kasar”
  • Kasar Sin Ta Taya Mahmoud Ali Youssouf Murnar Zabarsa Da Aka Yi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar AU
  • Iran: Himmati Yana Halattar Taro Dangane Da Matsalolin Da Suka Addabar Kasashe Masu Tasuwa
  • Shugaba Xi Ya Halarci Taron Kamfanoni Masu Zaman Kansu Tare Da Gabatar Da Jawabi