Aminiya:
2025-04-13@09:52:24 GMT

Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda

Published: 12th, February 2025 GMT

Fitaccen ɗan siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Abdulmajid Ɗan Bilki Kwamanda, ya ce ya yi nadamar mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a zaɓen 2023.

Yayin da yake zantawa da Aminiya ta wayar tarho, Kwamanda ya ce Shugaba Tinubu ya watsar da waɗanda suka sha wuya a kansa, duba da halin da ƙasa ke ciki a yanzu.

Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta

Ya bayyana cewa, a duk tsawon rayuwarsa, bai taɓa yin nadamar wani abu kamar yadda ya yi nadamar mara wa Tinubu baya ba.

“Da ciwo, amma dole a faɗi gaskiya. Ni cikakken ɗan jam’iyyar APC ne, amma dole na amince cewa gwamnatin APC ta gaza a wajen ‘yan Najeriya.

“Na sadaukar da lokaci da dukiyata wajen shawo kan mutane su zaɓi jam’iyyar, amma a yau ina nadamar hakan,” in ji shi.

Kwamanda, ya kuma nemi afuwar jama’a, inda ya bayyana cewa abubuwan da ya musu alƙawari a kai za a musu, gwamnatin APC ba ta cika ba.

“’Yan Najeriya na cikin yunwa kuma suna cikin fushi. Ba su da tabbas kan tsaro, kuma mulki ba ya tafiya daidai.

“Yawancin mutane ba sa iya cin abinci sau biyu a rana,” in ji shi.

Ɗan Bilki Kwamanda ya yi ƙaurin suna wajen suka da yin adawa mai zafi a tsakanin abokan hamayyar jam’iyyarsa a Jihar Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Bilki Kwamanda Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Wani Saɓani Tsakanin Tinubu Da Shettima — Jigon APC

Ya ce a siyasa akwai nau’ukan mutane uku – masu gaskiya, maƙaryata, da masu son tada zaune tsaye.

Ya ce su a matsayinsu na ‘ya’yan jam’iyyar APC na gaskiya, suna goyon bayan Tinubu da Shettima, kuma idan akwai kura-kurai, suna ganin ya kamata a gyara ne, ba a lalata komai ba.

Dangane da raɗe-raɗin cewa ana shirin sauya Shettima kafin zaɓen 2027, Jalo ya ce wannan ma labarin ƙanzon kurege ne.

Ya ce jam’iyya tana da hanyarta na sauya mutum, amma babu wani abu makamancin haka yanzu.

Ya ƙara da cewa suna jiran 2031 domin Shettima ya fito takarar shugaban ƙasa.

Har ila yau, ya buƙaci masu yaɗa jita-jita da su janye maganganunsu, su jira domin idan akwai matsala, za ta bayyana kanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Har Yanzu Shugabanci NNPP Na Hannunmu – Tsagin Kwankwaso
  • Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki NUPRC — Buba Galadima
  • Babu Wani Saɓani Tsakanin Tinubu Da Shettima — Jigon APC
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran
  • Trump ya janye harajin da ya kara wa duniya, amma ya laftawa China 125%