Leadership News Hausa:
2025-04-14@23:47:05 GMT

Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya

Published: 13th, February 2025 GMT

Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya

Har ila yau, ga irin su Apple, Microsoft, da Google da duk sun samu gindin zama a kasar Sin tare da bude ofisoshi da ressan masana’antu a biranen Shanghai, Beijing, da Shenzhen.

Haka nan sauran kamfanoni irin su Coca-Cola, da PepsiCo duk sun tsayu da kafafunsu sosai a kasar. Bugu da kari, ga kamfanonin harkokin biyan kudi ta fasahar zamani kamarsu Amazon da PayPal da su ma suka samu hadin kan kamfanonin kasar Sin don fadada kasuwancinsu a cikin kasar.

Duka wannan yana nuna yadda Sin ke fada da cikawa ne a kan manufofinta na kara bude kofa ga duniya. Kuma ya dace Amurka ta nuna sanin ya kamata a kan bahaguwar fahimtarta da sake lale kan matakanta na haddasa fitina a bangaren kasuwancin duniya.

Sannan ko da za ta nace a kan tana da ikon kara haraji a kan kayayyakin da ake shigo da su kasarta, to ta sani, ita ma tana da kamfanoni a kasashen waje da aka yi masu riga da wando, kuma masu karin magana sun ce, “ana barin halal don kunya!” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen

Jiragen yakin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan wasu yankunan a kasar Yemen a safiyar a jiya Asabar, wadanda suka Baida Sa’ada da kuma Hudaidah wadanda sune sake zafafa yaki a ciki kasar na baya-bayan nan.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kafafen yada labarai na kasar ta Yemen na fadar cewa jiragen yakin kasar ta Amurka sun kai  hare-hare har 5 a kan makarantar koyon sana’o’ii na Al-sawma  da ke lardin  Al-Bayda a jiya Asabar .

Labarin ya kara da cewa makarantar ita ce babbar makaranta a yankin, kuma cibiyar ilmi mafi girma. Har’ila yau labarin ya bayyana cewa jiragen yakin kasar ta Am,urka sun kai hare-hare har guda 3 a kan garin Al-Sahleen daga cikin yankunan Kitif da kuma Al-Bogee daga cikin lardin Sa’ada.

Labarin ya kara da cewa wannan yankin yana daga cikin yankunan da ake fafatawa da sojojin  Amurka, kuma suna yawaita kan hare-hare a cikinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamata Ya Yi Amurka Ta Kara Kokarin Gyara Kuskurenta 
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro