HausaTv:
2025-04-13@12:15:16 GMT

DRC : Kinshasa Ta Rufe Sararin Samaniyarta Ga Jiragen Rwanda

Published: 13th, February 2025 GMT

Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango ta yanke shawarar rufe sararin samaniyarta ga “dukkan jiragen sama na farar hula ko na gwamnati masu rijista dake zaune a Rwanda”.

A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Kwango, matakin ya “hana shawagi da sauka a cikin kasar ta Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, saboda dalilai na rashin tsaro da ke da nasaba da rikicin masu dauke da makamai.

A taswirorin zirga-zirgar jiragen sama na duniya, jiragen sama daga Kigali na kasar Rwanda, yanzu haka na kaucewa shiga sararin samaniyar Kongo.

Bayanai sun ce wani jirgin da ya tashi daga babban birnin kasar Rwanda zuwa birnin Landan na kasar Birtaniyaa ranar Talata, an tilas ya sauya hanyarsa don yin aiki da dokar, wanda a yanzu ya shafi “dukkan jiragen da suka yi rajista ko kuma suna zaune a Rwanda.”

A ranar Laraba, ma wasu jiragen Rwandair daga Kigali zuwa Libreville, Gabon, ko Lagos, Nigeria, suma sun yi zagaye don gujewa sararin samaniyar Kongo, lamarin daya shafi matafiya zuwa Libreville, da Najeriya wadanda suka samu karin sa’o’i uku na tafiya.

Ga kamfanonin da abin ya shafa, kuwa dokar zata tilasta musu karin kudin man fetur.

DR Kwango da Rwanda dai na takun tsaka game da rikin ‘yan tawayen M23 da Kinshassa ke zargin Kigali da goyan baya a rikicin gabashin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato

Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.

 Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.

Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.

A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.

Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.

Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”

Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Sin Za Ta Kara Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar Zuwa 125%
  • An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  •  Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen
  • Sojojin Sama Na HKI Kimani 1000 Guda New Suka Bukaci A Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865