HausaTv:
2025-02-20@08:59:00 GMT

DRC : Kinshasa Ta Rufe Sararin Samaniyarta Ga Jiragen Rwanda

Published: 13th, February 2025 GMT

Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango ta yanke shawarar rufe sararin samaniyarta ga “dukkan jiragen sama na farar hula ko na gwamnati masu rijista dake zaune a Rwanda”.

A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Kwango, matakin ya “hana shawagi da sauka a cikin kasar ta Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, saboda dalilai na rashin tsaro da ke da nasaba da rikicin masu dauke da makamai.

A taswirorin zirga-zirgar jiragen sama na duniya, jiragen sama daga Kigali na kasar Rwanda, yanzu haka na kaucewa shiga sararin samaniyar Kongo.

Bayanai sun ce wani jirgin da ya tashi daga babban birnin kasar Rwanda zuwa birnin Landan na kasar Birtaniyaa ranar Talata, an tilas ya sauya hanyarsa don yin aiki da dokar, wanda a yanzu ya shafi “dukkan jiragen da suka yi rajista ko kuma suna zaune a Rwanda.”

A ranar Laraba, ma wasu jiragen Rwandair daga Kigali zuwa Libreville, Gabon, ko Lagos, Nigeria, suma sun yi zagaye don gujewa sararin samaniyar Kongo, lamarin daya shafi matafiya zuwa Libreville, da Najeriya wadanda suka samu karin sa’o’i uku na tafiya.

Ga kamfanonin da abin ya shafa, kuwa dokar zata tilasta musu karin kudin man fetur.

DR Kwango da Rwanda dai na takun tsaka game da rikin ‘yan tawayen M23 da Kinshassa ke zargin Kigali da goyan baya a rikicin gabashin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba

Wasu daga cikin mutanen kasar Afirka ta kudu da suke dauke da cutar HIV suna yin koken cewa janye tallafin da Amurka ta yi a karkashin hukumar nan ta USAID, zai jefa rayuwarsu a tsakanin mutuwa da rayuwa.

Da akwai miliyoyin mutane a kasar ta Afirka Ta Kudu da suke dauke da cutar HIV da su ka cutu daga dakatar da ayyukan hukumar USAID akan  kiwon lafiya.

Yankin KwaZulu-Natal dake kasar Afirka ta kudu, yana da masu fama da cutar ta HIV da sun kai miliyan 1.9 a bisa kididdigar 2022. A fadin kasar kuwa da akwai masu dauke da wannan cutar da sun haura miliyan 7.5 da shi ne adadi mafi girma a duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama
  •  Rasha Ta Kakkabo Jiragen  Sama Marasa Matuki 9 Na Kasar Ukiraniya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
  • Kasar Iran Zata Aika Da Tawaga Mai Karfi Zuwa Jana’izar Sayyid Nasarallah
  • Sojojin HKI Sun Fara Ficewa Daga Wasu Wurare A Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojojin HKI Sun Ce Ba Zasu Fita Daga Wurare 5 A Kudancin Kasar Lebanon Ba
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Hamas Ta Sanar Da Shahadar Wani Jagoranta Da HKI Ta Kashe A Lebanon
  • Gobara ta yi ajalin uwa da ’ya’yanta a Ondo