HausaTv:
2025-02-20@08:51:35 GMT

Hamas Ta Yi Watsi Da Barazanar Amurka Da Isra’ila Kan Musayar Fursunoni

Published: 13th, February 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi watsi da barazanar da Isra’ila da Amurka ke yi kan batun musayar fursunoni.

Kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya fada cewa Isra’ila tana kaucewa aiwatar da wasu tanade-tanade na yarjejeniyar tsagaita bude wuta,” yana mai gargadin cewa ba za a sako mutanen da ake garkuwa da su ba idan ba Isra’ila ta mutunta yarjejeniyar ba.

Qassem ya ce, “Matsayinmu a fili yake, kuma ba za mu amince da barazanar Amurka da Isra’ila ba,” in ji Qassem, bayan firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu ya yi barazanar komwa yaki idan har ba a sako mutanen da aka kama ba zuwa ranar Asabar.

A ranar Laraba, ministan harkokin soji na gwamnatin ya yi gargadin cewa Isra’ila za ta sake fara yakin Gaza idan Hamas ta gaza sakin ‘yan Isra’ila da take tsare da su kuma a wannan karon za ta yi barna.

“Sabon yakin na Gaza zai sha bamban kuma mai tsanani da wanda ya gabata kafin tsagaita bude wuta, kuma ba zai kare ba sai mun fatattaki Hamas da kuma sako dukkan mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji Isra’ila Katz a cikin wata sanarwa.

“Hakan kuma zai ba da damar tabbatar shirin shugaban Amurka Donald Trump game da Gaza,” in ji Katz, yayin da yake magana kan shirin shugaban Amurka na mamaye yankin Falasdinu.

A baya dai kungiyar Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, wata tawaga karkashin jagorancin babban mai shiga tsakani ta isa birnin Alkahira inda ta fara ganawa da jami’an Masar” suna sa ido kan yadda ake aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yanayin tattalin arziki da ma wasu dalilai kan tilasta wa mutane da dama, ciki har da masu karɓar albashi a karshen wata, neman wata hanya ta daban dake kawo Karin kudade.

Shin mene ne yake kawo hakan, kuma mene ne tasirinsa a kan rayuwar masu buga-bugar da ma al’umma?

NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne a kan irin buga-bugar da ’yan Najeriya suke yi don sama wa kansu mafita.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda
  • Kasar Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Sun Baiwa Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Damar Ya Aikata Abin Da Yake So
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Hamas Ta Yabawa Tarayyar Afirka Kan Yin Tir Da Kisan Kare Dangin Isra’ila A Gaza
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
  • Amurka Da Isra’ila Sun Sake Barazanar ‘Lugudan Wuta’ A Gaza